< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
E proseguiu Job em proferir o seu dito, e disse:
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
Vive Deus, que desviou a minha causa, e o Todo-poderoso, que amargurou a minha alma.
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
Que, enquanto em mim houver alento, e o sopro de Deus nos meus narizes,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
Não falarão os meus lábios iniquidade, nem a minha língua pronunciará engano.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
Longe de mim que eu vos justifique: até que eu expire, nunca apartarei de mim a minha sinceridade.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
A minha justiça me apegarei e não a largarei: não me remorderá o meu coração em toda a minha vida.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Seja como o ímpio o meu inimigo, e o que se levantar contra mim como o perverso.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
Porque qual será a esperança do hipócrita, havendo sido ávaro, quando Deus lhe arrancar a sua alma?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Porventura Deus ouvirá o seu clamor, sobrevindo-lhe a tribulação?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Ou deleitar-se-á no Todo-poderoso? ou invocará a Deus em todo o tempo?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
Ensinar-vos-ei acerca da mão de Deus, e não vos encobrirei o que está com o Todo-poderoso.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Eis que todos vós já o vistes: porque pois vos desvaneceis na vossa vaidade?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
Esta pois é a porção do homem ímpio para com Deus, e a herança, que os tiranos receberão do Todo-poderoso.
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
Se os seus filhos se multiplicarem, será para a espada, e os seus renovos se não fartarão de pão.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
Os que ficarem dele na morte serão enterrados, e as suas viúvas não chorarão.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Se amontoar prata como pó, e aparelhar vestidos como lodo;
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
Ele os aparelhará, porém o justo os vestirá, e o inocente repartirá a prata.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
E edificará a sua casa como a traça, e como o guarda que faz a cabana.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
Rico se deita, e não será recolhido: seus olhos abre, e ele não será.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Pavores se apoderam dele como águas: de noite o arrebatará a tempestade.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
O vento oriental o levará, e ir-se-á, e o tempestuoso o arrebatará do seu lugar.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
E Deus lançará isto sobre ele, e não lhe poupará; irá fugindo da sua mão.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
Cada um baterá contra ele as palmas das mãos, e do seu lugar o assobiará.

< Ayuba 27 >