< Ayuba 27 >

1 Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
Moreouer Iob proceeded and continued his parable, saying,
2 “Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
The liuing God hath taken away my iudgement: for the Almightie hath put my soule in bitternesse.
3 Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
Yet so long as my breath is in me, and the Spirit of God in my nostrels,
4 bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
My lips surely shall speake no wickednesse, and my tongue shall vtter no deceite.
5 Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
God forbid, that I should iustifie you: vntill I dye, I will neuer take away mine innocencie from my selfe.
6 Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
I will keepe my righteousnesse, and wil not forsake it: mine heart shall not reprooue me of my dayes.
7 “Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
Mine enemie shall be as the wicked, and he that riseth against me, as the vnrighteous.
8 Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
For what hope hath the hypocrite when he hath heaped vp riches, if God take away his soule?
9 Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
Will God heare his cry, when trouble commeth vpon him?
10 Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
Will he set his delight on the Almightie? will he call vpon God at all times?
11 “Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
I will teache you what is in the hande of God, and I wil not conceale that which is with the Almightie.
12 Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
Beholde, all ye your selues haue seene it: why then doe you thus vanish in vanitie?
13 “Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
This is the portion of a wicked man with God, and the heritage of tyrants, which they shall receiue of the Almightie.
14 Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
If his children be in great nomber, the sworde shall destroy them, and his posteritie shall not be satisfied with bread.
15 Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
His remnant shall be buried in death, and his widowes shall not weepe.
16 Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
Though he shoulde heape vp siluer as the dust, and prepare rayment as the clay,
17 abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
He may prepare it, but the iust shall put it on, and the innocent shall deuide the siluer.
18 Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
He buildeth his house as the moth, and as a lodge that the watchman maketh.
19 Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
When the rich man sleepeth, he shall not be gathered to his fathers: they opened their eyes, and he was gone.
20 Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
Terrours shall take him as waters, and a tempest shall cary him away by night.
21 Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
The East winde shall take him away, and he shall depart: and it shall hurle him out of his place.
22 Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
And God shall cast vpon him and not spare, though he would faine flee out of his hand.
23 Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”
Euery man shall clap their hands at him, and hisse at him out of their place.

< Ayuba 27 >