< Ayuba 22 >

1 Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
And Eliphaz the Temanite answereth and saith: —
2 “Mutum yana iya zama da amfani a wurin Allah? Mai hikima ma zai iya zama da amfani a wurin shi?
To God is a man profitable, Because a wise man to himself is profitable?
3 Wane daɗi Allah zai ji in kai mai adalci ne? Wace riba zai samu in rayuwarka marar laifi ce?
Is it a delight to the Mighty One That thou art righteous? is it gain, That thou makest perfect thy ways?
4 “Ko don kana tsoron Allah shi ya sa ya kwaɓe ka ya kuma bari haka yă same ka?
Because of thy reverence Doth He reason [with] thee? He entereth with thee into judgment:
5 Ba muguntarka ce ta yi yawa ba? Ba zunubanka ne ba iyaka ba?
Is not thy wickedness abundant? And there is no end to thine iniquities.
6 Ka sa ɗan’uwanka yă biya ka bashin da kake binsa ba dalili; ka ƙwace wa mutanen rigunansu ka bar su tsirara.
For thou takest a pledge of thy brother for nought, And the garments of the naked Thou dost strip off.
7 Ba ka ba masu jin ƙishirwa su sha ba kuma ka hana wa masu jin yunwa abinci su ci.
Thou causest not the weary to drink water, And from the hungry thou withholdest bread.
8 Ko da yake kai mai ƙarfi ne, ka mallaki ƙasa, mutum mai martaba kuma, kana zama cikin ƙasarka.
As to the man of arm — he hath the earth, And the accepted of face — he dwelleth in it.
9 Ka kori gwauraye hannu wofi, ka kuma karya ƙarfin marayu.
Widows thou hast sent away empty, And the arms of the fatherless are bruised.
10 Shi ya sa kake kewaye da tarkuna, shi ya sa ka cika da tsoron mugun abin da zai auko maka.
Therefore round about thee [are] snares, And trouble thee doth fear suddenly.
11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, shi ya sa ambaliyar ruwa ta rufe ka.
Or darkness — thou dost not see, And abundance of waters doth cover thee.
12 “Ba Allah ne a can sama ba? Dubi yadda taurarin sama suke can nesa a sama!
Is not God high [in] heaven? And see the summit of the stars, That they are high.
13 Duk da haka ka ce, ‘Me Allah ya sani? A cikin duhu ne yake shari’a?
And thou hast said, 'What — hath God known? Through thickness doth He judge?
14 Gajimare ya rufe shi, saboda haka ba ya ganinmu lokacin da yake takawa a cikin sammai.’
Thick clouds [are] a secret place to Him, And He doth not see;' And the circle of the heavens He walketh habitually,
15 Za ka ci gaba da bin tsohuwar hanyar da mugayen mutane suka bi?
The path of the age dost thou observe, That men of iniquity have trodden?
16 An ɗauke su kafin lokacinsu yă cika, ruwa ya share tushensu.
Who have been cut down unexpectedly, A flood is poured out on their foundation.
17 Suka ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu! Me Maɗaukaki zai yi mana?’
Those saying to God, 'Turn aside from us,' And what doth the Mighty One to them?
18 Duk da haka kuwa shi ne ya cika gidajensu da abubuwa masu kyau, saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
And he hath filled their houses [with] good: (And the counsel of the wicked Hath been far from me.)
19 “Masu adalci suna gani ana hallaka mugaye, suna jin daɗi; marasa laifi suna yi musu ba’a, suna cewa,
See do the righteous and they rejoice, And the innocent mocketh at them,
20 ‘Ba shakka an hallaka maƙiyanmu, wuta kuma ta ƙona dukiyarsu.’
'Surely our substance hath not been cut off, And their excellency hath fire consumed.'
21 “Ka miƙa kanka ga Allah ka samu salamarsa; ta haka ne arziki zai zo maka.
Acquaint thyself, I pray thee, with Him, And be at peace, Thereby thine increase [is] good.
22 Ka bi umarnin da zai fito daga bakinsa kuma ka riƙe maganarsa a cikin zuciyarka.
Receive, I pray thee, from His mouth a law, And set His sayings in thy heart.
23 In ka komo ga Maɗaukaki, za ka warke. In ka kawar da mugunta daga cikin gidanka.
If thou dost return unto the Mighty Thou art built up, Thou puttest iniquity far from thy tents.
24 Ka jefar da zinariyarka a ƙasa, ka jefar da zinariyar Ofir da ka fi so a cikin duwatsu,
So as to set on the dust a defence, And on a rock of the valleys a covering.
25 sa’an nan ne Maɗaukaki zai zama zinariyarka, zai zama azurfa mafi kyau a wurinka.
And the Mighty hath been thy defence, And silver [is] strength to thee.
26 Ba shakka a lokacin ne za ka sami farin ciki daga wurin Maɗaukaki, ku kuma ɗaga idanunku ga Allah
For then on the Mighty thou delightest thyself, And dost lift up unto God thy face,
27 Za ka yi addu’a zuwa gare shi, zai kuwa ji ka, kuma za ka cika alkawuranka.
Thou dost make supplication unto Him, And He doth hear thee, And thy vows thou completest.
28 Abin da ka zaɓa za ka yi za ka yi nasara a ciki, haske kuma zai haskaka hanyarka.
And thou decreest a saying, And it is established to thee, And on thy ways hath light shone.
29 Sa’ad da aka ƙasƙantar da mutane ka kuma ce, ‘A ɗaga su!’ Sa’an nan zai ceci masu tawali’u.
For they have made low, And thou sayest, 'Lift up.' And the bowed down of eyes he saveth.
30 Zai ceci wanda ma yake mai laifi, wanda zai tsirar da shi ta wurin tsabtar hannuwanka.”
He delivereth the not innocent, Yea, he hath been delivered By the cleanness of thy hands.

< Ayuba 22 >