< Ayuba 21 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Hiob antwortete und sprach:
2 “Ku saurare ni da kyau; bari wannan yă zama ta’aziyyar da za ku ba ni.
Hört doch meiner Rede zu und laßt mir das anstatt eurer Tröstungen sein!
3 Ku ba ni zarafi in yi magana, bayan na gama sai ku yi ba’arku.
Vertragt mich, daß ich auch rede, und spottet darnach mein!
4 “A wurin mutum ne na kawo kukana? Don me ba zan kāsa haƙuri ba?
Handle ich denn mit einem Menschen? oder warum sollte ich ungeduldig sein?
5 Ku dube ni, ku kuma yi mamaki; ku rufe bakina da hannunku.
Kehrt euch her zu mir; ihr werdet erstarren und die Hand auf den Mund legen müssen.
6 Lokacin da na yi tunanin wannan, sai in ji tsoro; jikina yă fara rawa.
Wenn ich daran denke, so erschrecke ich, und Zittern kommt mein Fleisch an.
7 Don me mugaye suke rayuwa har su tsufa, suna kuma ƙaruwa da iko?
Warum leben denn die Gottlosen, werden alt und nehmen zu an Gütern?
8 Suna ganin’ya’yansu suna girma, suna ganin jikokinsu suna tasowa a kan idanunsu.
Ihr Same ist sicher um sie her, und ihre Nachkömmlinge sind bei ihnen.
9 Gidajensu suna zama cikin lafiya ba ruwansu da fargaba. Kuma Allah ba ya ba su horo.
Ihr Haus hat Frieden vor der Furcht, und Gottes Rute ist nicht über ihnen.
10 Shanunsu ba sa fasa haihuwa; suna haihuwa ba sa yin ɓari.
Seinen Stier läßt man zu, und es mißrät ihm nicht; seine Kuh kalbt und ist nicht unfruchtbar.
11 Suna aika’ya’yansu kamar garke;’ya’yansu suna guje-guje da tsalle-tsalle.
Ihre jungen Kinder lassen sie ausgehen wie eine Herde, und ihre Knaben hüpfen.
12 Suna rera da kayan kiɗa na ganga da garaya; suna jin daɗin busar sarewa.
Sie jauchzen mit Pauken und Harfen und sind fröhlich mit Flöten.
13 Suna yin rayuwarsu cikin arziki kuma su mutu cikin salama. (Sheol h7585)
Sie werden alt bei guten Tagen und erschrecken kaum einen Augenblick vor dem Tode, (Sheol h7585)
14 Duk da haka suna ce wa Allah, ‘Ka rabu da mu.’ Ba ma so mu san hanyoyinka.
die doch sagen zu Gott: “Hebe dich von uns, wir wollen von deinen Wegen nicht wissen!
15 Wane ne Maɗaukaki har da za mu bauta masa? Wace riba za mu samu ta wurin yin addu’a gare shi?
Wer ist der Allmächtige, daß wir ihm dienen sollten? oder was sind wir gebessert, so wir ihn anrufen?”
16 Amma arzikinsu ba a hannunsu yake ba saboda haka ba ruwana da shawarar mugaye.
“Aber siehe, ihr Glück steht nicht in ihren Händen; darum soll der Gottlosen Sinn ferne von mir sein.”
17 “Duk da haka, sau nawa fitilar mugu take mutuwa? Sau nawa bala’i yake auka masa, ko Allah ya taɓa hukunta mugu cikin fushi?
Wie oft geschieht's denn, daß die Leuchte der Gottlosen verlischt und ihr Unglück über sie kommt? daß er Herzeleid über sie austeilt in seinem Zorn?
18 Sau nawa suke zama kamar tattaka a iska, ko kuma kamar ƙura da iskar hadari take kwashewa?
daß sie werden wie Stoppeln vor dem Winde und wie Spreu, die der Sturmwind wegführt?
19 An ce ‘Allah yana tara wa’ya’yan mutum horon da zai ba mutumin.’ Bari yă ba mutumin horo don yă san ya yi haka!
“Gott spart desselben Unglück auf seine Kinder”. Er vergelte es ihm selbst, daß er's innewerde.
20 Bari idanunsa su ga yadda zai hallaka; bari yă sha daga fushin Maɗaukaki.
Seine Augen mögen sein Verderben sehen, und vom Grimm des Allmächtigen möge er trinken.
21 Ko zai damu da iyalin da ya bari a baya sa’ad da kwanakinsa suka ƙare?
Denn was ist ihm gelegen an seinem Hause nach ihm, wenn die Zahl seiner Monden ihm zugeteilt ist?
22 “Wani zai iya koya wa Allah ilimi tun da yana shari’anta har da waɗanda suke manya masu iko?
Wer will Gott lehren, der auch die Hohen richtet?
23 Wani mutum zai mutu cikin jin daɗi da kwanciyar hankali,
Dieser stirbt frisch und gesund in allem Reichtum und voller Genüge,
24 jikinsa ɓulɓul, ƙasusuwansa da alamar ƙarfi.
sein Melkfaß ist voll Milch, und seine Gebeine werden gemästet mit Mark;
25 Wani kuma zai mutu cikin ɗacin rai, bai taɓa jin daɗin wani abu mai kyau ba.
jener aber stirbt mit betrübter Seele und hat nie mit Freuden gegessen;
26 Dukansu kuwa za a bizne su a ƙasa, kuma tsutsotsi za su cinye su.
und liegen gleich miteinander in der Erde, und Würmer decken sie zu.
27 “Na san duk abin da kuke tunani, yadda za ku saɓa mini.
Siehe, ich kenne eure Gedanken wohl und euer frevles Vornehmen gegen mich.
28 Kuna cewa, ‘Yanzu ina gidan babban mutumin nan, tenti wurin da mugaye suke zama?’
Denn ihr sprecht: “Wo ist das Haus des Fürsten? und wo ist die Hütte, da die Gottlosen wohnten?”
29 Ba ku taɓa tambayar waɗanda suke tafiya ba? Ba ku kula da labaransu,
Habt ihr denn die Wanderer nicht befragt und nicht gemerkt ihre Zeugnisse?
30 cewa an kāre mugu daga ranar bala’i, an kāre shi daga ranar fushi?
Denn der Böse wird erhalten am Tage des Verderbens, und am Tage des Grimms bleibt er.
31 Wane ne yake gaya masa abin da ya yi? Wane ne yake rama abin da ya yi?
Wer will ihm ins Angesicht sagen, was er verdient? wer will ihm vergelten, was er tut?
32 Za a bizne shi a kabari, a kuma yi tsaron kabarinsa.
Und er wird zu Grabe geleitet und hält Wache auf seinem Hügel.
33 Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali; dukan jama’a suna binsa, da yawa kuma suna gabansa.
Süß sind ihm die Schollen des Tales, und alle Menschen ziehen ihm nach; und derer, die ihm vorangegangen sind, ist keine Zahl.
34 “Saboda haka ta yaya za ku iya yi mini ta’aziyya da surutan banzan nan naku? Babu wani abu cikin amsarku sai ƙarya!”
Wie tröstet ihr mich so vergeblich, und eure Antworten finden sich unrecht!

< Ayuba 21 >