< Ayuba 20 >

1 Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
Then Zophar the Naamathite answered,
2 “Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
“Therefore my thoughts answer me, even by reason of my haste that is in me.
3 Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
I have heard the reproof which puts me to shame. The spirit of my understanding answers me.
4 “Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
Don’t you know this from old time, since man was placed on earth,
5 mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
that the triumphing of the wicked is short, the joy of the godless but for a moment?
6 Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
Though his height mount up to the heavens, and his head reach to the clouds,
7 Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
yet he will perish forever like his own dung. Those who have seen him will say, ‘Where is he?’
8 Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
He will fly away as a dream, and will not be found. Yes, he will be chased away like a vision of the night.
9 Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
The eye which saw him will see him no more, neither will his place see him any more.
10 Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
His children will seek the favour of the poor. His hands will give back his wealth.
11 Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
His bones are full of his youth, but youth will lie down with him in the dust.
12 “Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
“Though wickedness is sweet in his mouth, though he hide it under his tongue,
13 ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
though he spare it, and will not let it go, but keep it still within his mouth,
14 duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
yet his food in his bowels is turned. It is cobra venom within him.
15 Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
He has swallowed down riches, and he will vomit them up again. God will cast them out of his belly.
16 Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
He will suck cobra venom. The viper’s tongue will kill him.
17 Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
He will not look at the rivers, the flowing streams of honey and butter.
18 Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
He will restore that for which he laboured, and will not swallow it down. He will not rejoice according to the substance that he has gotten.
19 Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
For he has oppressed and forsaken the poor. He has violently taken away a house, and he will not build it up.
20 “Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
“Because he knew no quietness within him, he will not save anything of that in which he delights.
21 Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
There was nothing left that he didn’t devour, therefore his prosperity will not endure.
22 Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
In the fullness of his sufficiency, distress will overtake him. The hand of everyone who is in misery will come on him.
23 Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
When he is about to fill his belly, God will cast the fierceness of his wrath on him. It will rain on him while he is eating.
24 Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
He will flee from the iron weapon. The bronze arrow will strike him through.
25 Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
He draws it out, and it comes out of his body. Yes, the glittering point comes out of his liver. Terrors are on him.
26 duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
All darkness is laid up for his treasures. An unfanned fire will devour him. It will consume that which is left in his tent.
27 Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
The heavens will reveal his iniquity. The earth will rise up against him.
28 Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
The increase of his house will depart. They will rush away in the day of his wrath.
29 Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”
This is the portion of a wicked man from God, the heritage appointed to him by God.”

< Ayuba 20 >