< Ayuba 19 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Then Job answered,
2 “Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
"How long will you torment me, and crush me with words?
3 Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
You have reproached me ten times. You aren't ashamed that you attack me.
4 In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
If it is true that I have erred, my error remains with myself.
5 In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
If indeed you will magnify yourselves against me, and plead my disgrace against me;
6 sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
know now that God has subverted me, and has surrounded me with his net.
7 “Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
"Look, I cry out 'Injustice.' but there is no justice.
8 Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
He has walled up my way so that I can't pass, and has set darkness in my paths.
9 Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
He has stripped me of my glory, and taken the crown from my head.
10 Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
He has broken me down on every side, and I am gone. My hope he has plucked up like a tree.
11 Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
He has also kindled his wrath against me. He counts me among his adversaries.
12 Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
His troops come on together, build a siege ramp against me, and camp around my tent.
13 “Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
"He has put my brothers far from me. My acquaintances are wholly estranged from me.
14 Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
My relatives have gone away. My familiar friends have forgotten me.
15 Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
Those who dwell in my house, and my maids, count me for a stranger. I am a foreigner in their sight.
16 Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
I call to my servant, and he gives me no answer. I beg him with my mouth.
17 Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
My breath is offensive to my wife. I am loathsome to the children of my own mother.
18 Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
Even young children despise me. If I arise, they speak against me.
19 Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
All my familiar friends abhor me. They whom I loved have turned against me.
20 Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
My bones stick to my skin and to my flesh. I have escaped by the skin of my teeth.
21 “Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
"Have pity on me, have pity on me, you my friends; for the hand of God has touched me.
22 Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
Why do you persecute me as God, and are not satisfied with my flesh?
23 “Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
"Oh that my words were now written. Oh that they were inscribed in a scroll.
24 a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
That with an iron pen and lead they were engraved in the rock forever.
25 Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
But as for me, I know that my Redeemer lives. In the end, he will stand upon the earth.
26 Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
After my skin is destroyed, then in my flesh shall I see God,
27 Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
Whom I, even I, shall see on my side. My eyes shall see, and not as a stranger. My heart is consumed within me.
28 “In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
If you say, 'How we will persecute him, because the root of the matter is found in him.'
29 sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”
Be afraid of the sword, for wrath brings the punishments of the sword, that you may know there is a judgment."

< Ayuba 19 >