< Ayuba 16 >

1 Sai Ayuba ya amsa,
Alors Job prit la parole et dit:
2 “Na ji abubuwa da yawa kamar waɗannan; dukanku ba ku iya ta’aziyya ba!
J'ai souvent entendu de semblables harangues; vous êtes tous d'insupportables consolateurs.
3 Dogayen surutanku ba sa ƙare ne? Me yake sa kuke ta yin waɗannan surutai har kuke cin gaba da yin gardama?
Quand finiront ces vains discours? Quel aiguillon t'excite à répliquer?
4 Ni ma zan iya yin maganganu kamar yadda kuke yi in da kuna cikin halin da nake; zan iya faɗar duk abubuwan da kuke faɗi, in kaɗa muku kaina.
Moi aussi, je saurais parler comme vous, si vous étiez à ma place; j'arrangerais de beaux discours à votre adresse, je secouerais la tête sur vous;
5 Amma bakina zai ƙarfafa ku; ta’aziyyar da za tă fito daga bakina za tă kawar muku da ɓacin zuciyarku.
je vous encouragerais de la bouche, et vous auriez pour soulagement l'agitation de mes lèvres.
6 “Duk da haka in na yi magana, ba na samun sauƙi; in ma na yi shiru zafin ba ya tafiya.
Si je parle, ma douleur n'est pas adoucie; si je me tais, en est-elle soulagée?
7 Ba shakka ya Allah ka gajiyar da ni; ka ɓata gidana gaba ɗaya.
Aujourd'hui, hélas! Dieu a épuisé mes forces... ô Dieu, tu as moissonné tous mes proches.
8 Ka daure ni, ya kuma zama shaida; yadda na rame sai ƙasusuwa, wannan ya sa ake gani kamar don ni mai zunubi ne shi ya sa.
Tu me garrottes... c'est un témoignage contre moi!... ma maigreur se lève contre moi, en face elle m'accuse.
9 Allah ya kai mini hari ya yi kaca-kaca da ni cikin fushinsa yana cizon haƙoransa don fushin da yake yi da ni; ya zura mini ido.
Sa colère me déchire et me poursuit, il grince des dents contre moi; mon ennemi darde sur moi ses regards.
10 Mutane suka buɗe baki suka yi mini riyar reni; suka yi mini ba’a suka haɗu suka tayar mini.
Ils ouvrent leur bouche pour me dévorer, ils me frappent la joue avec outrage, ils se liguent tous ensemble pour me perdre.
11 Allah ya bashe ni ga mugayen mutane, ya jefa ni hannun mugaye.
Dieu m'a livré au pervers, il m'a jeté entre les mains des méchants.
12 Dā ina zamana lafiya kome yana tafiya daidai; amma ya ragargaza ni; ya shaƙe ni a wuya; ya murƙushe ni na zama abin barata gare shi;
J'étais en paix, et il m'a secoué, il m'a saisi par la nuque, et il m'a brisé. Il m'a posé en but à ses traits,
13 maharbansa sun kewaye ni. Ba tausayi, ya soke ni a ƙodata har jini ya zuba a ƙasa.
ses flèches volent autour de moi; il perce mes flancs sans pitié, il répand mes entrailles sur la terre;
14 Ya ji mini rauni a kai a kai ya auko mini kamar mai yaƙi.
il me fait brèche sur brèche, il fond sur moi comme un géant.
15 “Ina makoki saye da tsummoki na ɓoye fuskata a cikin ƙura.
J'ai cousu un sac sur ma peau, et j'ai roulé mon front dans la poussière.
16 Fuskata ta yi ja don kuka idanuna sun kukumbura;
Mon visage est tout rouge de larmes, et l'ombre de la mort s'étend sur mes paupières,
17 duk da haka hannuwana ba su aikata ɓarna ba kuma addu’ata mai tsabta ce.
quoiqu'il n'y ait pas d'iniquités dans mes mains, et que ma prière soit pure.
18 “Ya duniya, kada ki ɓoye jinina; bari yă yi kuka a madadina!
O terre, ne couvre point mon sang, et que mes cris s'élèvent librement!
19 Ko yanzu haka shaidata tana sama; wanda zai tsaya mini yana sama.
A cette heure même, voici que j'ai mon témoin dans le ciel, mon défenseur dans les hauts lieux.
20 Shi mai yin roƙo a madadina abokina ne yayinda nake kuka ga Allah;
Mes amis se moquent de moi, c'est vers Dieu que pleurent mes yeux.
21 a madadin mutum ya yi roƙo ga Allah kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa.
Qu'il juge lui-même entre Dieu et l'homme, entre le fils de l'homme et son semblable!
22 “Shekaru kaɗan suka rage in kama hanyar da ba a komawa.
Car les années qui me sont comptés s'écoulent, et j'entre dans un sentier d'où je ne reviendrai pas.

< Ayuba 16 >