< Ayuba 10 >

1 “Na gaji da rayuwa; saboda haka bari in faɗi zuciyata gabagadi yadda raina yake jin ba daɗi.
My soul doth loathe my life, —I let loose my complaint, I speak, in the bitterness of my soul.
2 Zan ce wa Allah, kada ka hukunta ni, amma ka gaya mini laifin da na yi maka.
I say unto GOD, Do not hold me guilty, Let me know, on what account thou contendest with me!
3 Kana jin daɗin ba ni wahala, don me ka yashe ni, abin da ka halitta da hannunka, yayinda kake murmushi game da shirye-shiryen mugaye?
Is it seemly in thee, that thou shouldst oppress? that thou shouldst despise the labour of thine own hand, when, upon the counsel of the lawless, thou hast shone?
4 Idanunka irin na mutum ne? Kana gani yadda mutum yake gani ne?
Eyes of flesh, hast thou? or, as a mortal seeth, seest thou?
5 Kwanakinka kamar na mutane ne, ko shekarunka kamar na mutane ne
As the days of a mortal, are thy days? or, thy years, as the days of a man?
6 da za ka neme ni da laifi ka hukunta ni?
That thou shouldst seek for mine iniquity, and, for my sin, shouldst make search:
7 Ko da yake ka san ba ni da laifi, kuma ba wanda zai iya cetona daga hannunka.
Though it is, within thine own knowledge, that I would not be lawless, and, none, out of thy hand, can deliver?
8 “Da hannuwanka ka ƙera ni, kai ka halicce ni. Yanzu kuma kai za ka juya ka hallaka ni?
Thine own hands, shaped me, and made me, all in unison round about, and yet thou hast confounded me.
9 Ka tuna cewa ka mulmula ni kamar yumɓu. Yanzu za ka mai da ni in zama ƙura kuma?
Remember, I pray thee, that, as clay, thou didst make me, and, unto dust, thou wilt cause me to return.
10 Ba kai ka zuba ni kamar madara ba, na daskare kamar cuku.
Didst thou not, like milk, pour me forth? and, as cheese, curdle me?
11 Ka rufe ni da tsoka da fata, ka harhaɗa ni da ƙasusuwa da jijiyoyi?
With skin and flesh, clothe me? and, with bones and sinews, interweave me?
12 Ka ba ni rai ka kuma yi mini alheri, kuma cikin tanadinka ka kula da ruhuna.
Life and lovingkindness, thou didst bestow upon me, —and, thy watchful care, preserved my breath.
13 “Amma wannan shi ne abin da ka ɓoye a zuciyarka, na kuma san abin da yake cikin zuciyarka ke nan.
Yet, these things, thou didst hide in thy heart, I know that, this, hath been with thee!
14 In na yi zunubi kana kallo na kuma ba za ka fasa ba ni horo ba don laifin da na yi.
If I have sinned, then couldst thou watch me, and, from mine iniquity, thou wouldst not acquit me:
15 Idan ina da laifi, kaitona! Ko da ba ni da laifi, ba zan iya ɗaga fuskata ba, gama kunya ta ishe ni duk ɓacin rai ya ishe ni.
If I have been lawless, alas for me! Or, if I am righteous, I will not lift up my head, Surfeited with shame, look thou then on my humiliation.
16 In na ɗaga kaina, za ka neme ni kamar zaki ka sāke nuna al’ajabin ikonka a kaina.
When it is lifted up, like a howling lion, thou dost hunt me, Then again thou dost shew thyself marvellous against me.
17 Kana sāke kawo sababbin waɗanda za su ba da shaida a kaina kana ƙara haushinka a kaina; kana ƙara kawo mini hari.
Thou renewest thy witnesses before me, and dost increase thy vexation with me, Relays—yea an army, is with me.
18 “Me ya sa ka fito da ni daga cikin uwata? Da ma na mutu kafin a haife ni.
Wherefore then, from the womb, didst thou bring me forth? I might have breathed my last, and, no eye, have seen me.
19 Da ma ba a halicce ni ba, da na mutu tun daga cikin cikin uwata na wuce zuwa kabari!
As though I had not been, should I have become, —from the womb to the grave, might I have been borne.
20 ’Yan kwanakina ba su kusa ƙarewa ba ne? Ka rabu da ni don in ɗan samu sukuni na ɗan lokaci
Are not my days, few?—then forbear, and set me aside, that I may brighten up for a little;
21 kafin in koma inda na fito, ƙasa mai duhu da inuwa sosai,
Before I go, and not return, unto a land of darkness and death-shade:
22 zuwa ƙasa mai duhun gaske, da inuwa da hargitsi, inda haske yake kamar duhu.”
A land of obscurity, like thick darkness, of death-shade and disorder, and which shineth like thick darkness.

< Ayuba 10 >