< Irmiya 5 >

1 “Ku yi ta kai da kawowa a titunan Urushalima, ku dudduba ko’ina ku kuma lura, ku bincika cikin dandalinta. Ko za ku sami mutum guda wanda yake aikata adalci wanda yake kuma son bin gaskiya, sai in gafarta wa wannan birni.
Parcourez les rues de Jérusalem et regardez, informez-vous; cherchez sur ses places publiques si vous y trouvez un homme, s'il en est un qui pratique la justice, et qui recherche la fidélité, et je ferai grâce à la ville.
2 Ko da yake suna cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye,’ duk da haka suna rantsuwar ƙarya.”
Même quand ils disent: " Yahweh est vivant! " c'est pour le mensonge qu'ils jurent.
3 Ya Ubangiji, idanunka ba sa ganin gaskiya? Ka buge su, amma ba su ji zafi ba; ka ragargaza su, amma suka ƙi su gyara. Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse suka ƙi su tuba.
Yahweh, vos yeux ne cherchent-ils pas la fidélité? Vous les avez frappés, et ils n'ont pas eu de douleur; vous les avez exterminés, et ils n'ont pas voulu recevoir l'instruction; ils ont endurci leur face plus que le roc; ils ont refusé de revenir.
4 Na yi tunani, “Waɗannan ne kawai matalauta; su wawaye ne, gama ba su san hanyar Ubangiji ba, ko abubuwan da Allahnsu yake bukata ba.
Et moi, je disais: Ce ne sont que les petits. Ils agissent en insensés, car ils ne savent pas la voie de Yahweh, la loi de leur Dieu.
5 Saboda haka zan tafi wurin shugabanni in yi musu magana; tabbatacce sun san hanyar Ubangiji, da abubuwan da Allahnsu yake bukata.” Amma da nufi guda su ma suka karye karkiyar suka tsintsinke sarƙoƙin.
J'irai donc vers les grands et je leur parlerai; car eux, ils savent la voie de Yahweh, La loi de leur Dieu... Mais eux aussi, ils ont tous ensemble brisé le joug, Rompu les liens!
6 Saboda haka zaki daga kurmi zai fāɗa musu, kyarkeci kuma daga hamada zai cinye su, damisa za tă yi musu ƙawanya kusa da garuruwansu yă yayyage duk wanda ya kuskura ya fita, gama tawayensu da girma yake jan bayansu kuma yana da yawa.
C'est pourquoi le lion de la forêt les a frappés, le loup du désert les ravage; la panthère est aux aguets devant leurs villes, tout homme qui en sort est déchiré; car leurs transgressions sont nombreuses, et leurs révoltes se sont accrues.
7 “Me zai sa in gafarta muku?’Ya’yanku sun yashe ni sun yi rantsuwa da allolin da ba alloli ba ne. Na biya musu dukan bukatunsu, duk da haka suka yi zina suka tattaru a gidajen karuwai.
Pour quelle raison te ferais-je grâce! Tes fils m'ont abandonné, et ils jurent par ce qui n'est pas Dieu. Je les ai rassasiés, et ils ont été adultères; ils vont par troupes dans la maison de la prostituée.
8 An ciyar da su sosai, kamar ƙosassun ingarmu, masu jaraba, kowanne yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa.
Etalons bien repus, vagabonds, chacun d'eux hennit à la femme de son prochain.
9 Ba zan hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’ummar nan ba?
Et je ne les punirais pas pour ces crimes! — oracle de Yahweh; et d'une nation telle que celle-là je ne me vengerais pas!
10 “Ku ratsa cikin gonakin inabinta ku cinye su, amma kada ku hallaka su gaba ɗaya. Ku kakkaɓe rassanta, gama waɗannan mutane ba na Ubangiji ba ne.
Escaladez ses murs et détruisez, mais non pas entièrement; enlevez ses sarments, car ils ne sont pas à Yahweh!
11 Gidan Isra’ila da gidan Yahuda sun zama marasa aminci gaba ɗaya gare ni” in ji Ubangiji.
Car elles m'ont été tout à fait infidèles, la maison d'Israël et la maison de Juda, — oracle de Yahweh.
12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji; sun ce, “Ba zai yi kome ba! Ba wata masifar da za tă same mu; ba za mu taɓa ganin takobi ko yunwa ba.
Ils ont renié Yahweh et dit: " Il n'est pas, et le malheur ne viendra pas sur nous; nous ne verrons ni l'épée, ni la famine.
13 Annabawa holoƙo ne kawai maganar kuwa ba ta cikinsu; saboda haka bari abin da suke faɗi ya koma kansu.”
Les prophètes ne sont que du vent, et personne ne parle en eux: qu'il leur soit fait ainsi à eux-mêmes! "
14 Saboda haka ga abin Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Domin mutanen sun yi waɗannan maganganu, zan mai da maganata a bakinku wuta waɗannan mutane kuwa su zama itacen da za tă ci.
C'est pourquoi ainsi parle Yahweh, le Dieu des armées: Parce que vous dites cette parole-là, voici que je mets ma parole dans ta bouche comme un feu, et ce peuple sera comme du bois et ce feu les dévorera.
15 Ya gidan Isra’ila,” in ji Ubangiji, “Ina kawo al’umma daga nesa a kanku al’umma ce ta tun dā mai ƙarfin hali, mutane ne da ba ku san harshensu ba, waɗanda ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba.
Me voici qui amène sur vous une nation qui vient de loin, maison d'Israël, — oracle de Yahweh; c'est une nation forte, c'est une nation antique, une nation dont tu ne connais pas la langue, et tu n’entends pas ce qu'elle dit.
16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne; dukansu jarumawa ne.
Son carquois est un sépulcre ouvert; ils sont tous des héros.
17 Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku, za su cinye’ya’yanku maza da mata; za su cinye garkunan tumakinku da na awakinku, za su cinye’ya’yan inabinku da na ɓaurenku. Da takobi za su hallaka biranenku masu katanga.
Elle dévorera ta moisson et ton pain; elle dévorera tes fils et tes filles; elle dévorera tes brebis et tes bœufs; elle dévorera ta vigne et ton figuier; elle détruira par l'épée tes villes fortes dans lesquelles tu te confies.
18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki,” in ji Ubangiji, “ba zan hallaka ku gaba ɗaya ba.
Mais même en ces jours-là, — oracle du Yahweh, je ne vous détruirai pas entièrement.
19 Sa’ad da kuma mutanen suka yi tambaya, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi dukan wannan gare mu?’ Sai ka amsa musu, ‘Yadda kuka yashe ni kuka kuma bauta wa baƙin alloli a ƙasarku, haka yanzu za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’
Et quand vous direz: " Pour quelle raison Yahweh, notre Dieu, nous a-t-il fait toutes ces choses? " Tu leur diras: " Comme vous m'avez abandonné pour servir dans votre pays un dieu étranger, ainsi vous servirez des étrangers dans un pays qui n'est pas à vous."
20 “Ka sanar da wannan ga gidan Yaƙub ka yi shelarsa a Yahuda.
Annoncez ceci dans la maison de Jacob; et publiez-le dans Juda, en ces termes:
21 Ku ji wannan, ku wawaye marasa azanci, waɗanda suke da idanu amma ba sa gani, waɗanda suke da kunnuwa amma ba sa ji.
Ecoutez donc ceci, peuple insensé et sans cœur! Ils ont des yeux et ne voient point, des oreilles et ils n'entendent point!
22 Bai kamata ku ji tsorona ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata ku yi rawar jiki a gabana ba? Na sa yashi ya zama iyakar teku, madawwamiyar iyakar da ba zai tsallake ba. Raƙuman ruwa za su iya yin hauka, amma ba za su iya haye ta ba; za su iya yin ruri, amma ba za su iya ƙetare ta ba.
Ne me craindrez-vous pas, — oracle de Yahweh; ne tremblerez-vous pas devant moi, moi qui ai mis le sable pour limite à la mer, borne éternelle, qu'elle ne franchira pas? Ses flots s'agitent, et ils sont impuissants; ils mugissent, et ils ne la dépassent pas.
23 Amma mutanen nan suna da tauraren zukata, kuma’yan tawaye ne; sun kauce suka kuma rabu da ni.
Mais ce peuple a un cœur indocile et rebelle; ils se retirent et s'en vont.
24 Ba sa faɗa wa kansu, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu, wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari na kaka da na bazara, wanda kullum yake tabbatar mana da girbi.’
Ils ne disent pas dans leur cœur: " Craignons Yahweh notre Dieu lui qui donne la pluie, celle de la première saison, et celle de l'arrière-saison en son temps, et qui nous garde les semaines destinées à la moisson. "
25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa; zunubanku sun hana ku samun alheri.
Vos iniquités ont dérangé cet ordre; vos péchés vous privent de ces biens.
26 “A cikin mutanena an sami mugaye waɗanda suke kwanton ɓauna kamar masu sa tarko wa tsuntsaye kamar waɗanda suke kafa tarko don su kama mutane.
Car il se trouve des pervers dans mon peuple; ils épient comme l'oiseleur qui se baisse, ils dressent des pièges et prennent des hommes.
27 Kamar keji cike da tsuntsaye, gidajensu sun cika da ruɗu; sun yi arziki suka kuma zama masu iko
Comme une cage est pleine d'oiseaux, ainsi leurs maisons sont pleines de fraude; aussi deviennent-ils puissants et riches;
28 suka kuma yi ƙiba, suka yi bul-bul. Mugayen ayyukansu ba su da iyaka; ba sa wa marayu shari’ar adalci, ba sa kāre’yancin matalauta.
Ils s'engraissent, ils reluisent. Ils dépassent même la mesure du mal; ils ne font pas justice, justice à l'orphelin... et ils prospèrent!... Ils ne font pas droit aux malheureux.
29 Bai kamata in hukunta su saboda wannan ba?” In ji Ubangiji. “Bai kamata in yi ramuwa a kan irin al’umma kamar wannan ba?
Et je ne punirais pas ces crimes! — oracle de Yahweh; et d'une nation telle que celle-là je ne me vengerais pas!...
30 “Abin banmamaki da bantsoro ya faru a ƙasar.
Des choses abominables, horribles, se font dans le pays.
31 Annabawa suna annabcin ƙarya, firistoci suna mulki da ikon kansu, mutanena kuma suna son haka. Amma me za ku yi a ƙarshe?
Les prophètes prophétisent en mentant, les prêtres gouvernent d'accord avec eux! Et mon peuple l'aime ainsi! Et que ferez-vous au terme de tout cela?

< Irmiya 5 >