< Irmiya 49 >

1 Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
Against the children of Ammon. Thus saith the Lord: Hath Israel no sons? or hath he no heir? Why then hath Melchom inherited Gad: and his people dwelt in his cities?
2 Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
Therefore behold the days come, saith the Lord, and I will cause the noise of war to be heard in Rabbath of the children of Ammon, and it shall be destroyed into a heap, and her daughters shall be burnt with fire, and Israel shall possess them that have possessed him, saith the Lord.
3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
Howl, O Hesebon, for Hai is wasted. Cry, ye daughters of Rabbath, gird yourselves with haircloth: mourn and go about by the hedges: for Melchom shall be carried into captivity, his priests, and his princes together.
4 Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
Why gloriest thou in the valleys? thy valley hath flowed away, O delicate daughter, that hast trusted in thy treasures, and hast said: Who shall come to me?
5 Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
Behold I will bring a fear upon thee, saith the Lord God of hosts, from all that are round about thee: and you shall be scattered every one out of one another’s sight, neither shall there be any to gather together them that flee.
6 “Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
And afterwards I will cause the captives of the children of Ammon to return, saith the Lord.
7 Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
Against Edom. Thus saith the Lord of hosts: Is wisdom no more in Theman? counsel is perished from her children: their wisdom is become unprofitable.
8 Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
Flee and turn your backs, go down into the deep hole, ye inhabitants of Dedan: for I have brought the destruction of Esau upon him, the time of his visitation.
9 In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
If grapegatherers had come to thee, would they not have left a bunch? if thieves in the night, they would have taken what was enough for them.
10 Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
But I have made Esau bare, I have revealed his secrets, and he cannot be hid: his seed is laid waste, and his brethren, and his neighbours, and he shall not be.
11 Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
Leave thy fatherless children: I will make them live: and thy widows shall hope in me.
12 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
For thus saith the Lord: Behold they whose judgment was not to drink of the cup, shall certainly drink: and shalt thou come off as innocent? thou shalt not come off as innocent, but drinking thou shalt drink.
13 Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
For I have sworn by myself, saith the Lord, that Bosra shall become a desolation, and a reproach, and a desert, and a curse: and all her cities shall be everlasting wastes.
14 Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
I have heard a rumour from the Lord, and an ambassador is sent to the nations: Gather yourselves together, and come against her, and let us rise up to battle.
15 “Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
For behold I have made thee a little one among the nations, despicable among men.
16 Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
Thy arrogancy hath deceived thee, and the pride of thy heart: O thou that dwellest in the clefts of the rock, and endeavourest to lay hold on the height of the hill: but though thou shouldst make thy nest as high as an eagle, I will bring thee down from thence, saith the Lord.
17 “Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
And Edom shall be desolate: every one that shall pass by it, shall be astonished, and shall hiss at all its plagues.
18 Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
As Sodom was overthrown and Gomorrha, and the neighbours thereof, saith the Lord: there shall not a man dwell there, and there shall no son of man inhabit it.
19 “Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
Behold one shall come up as a lion from the swelling of the Jordan, against the strong and beautiful: for I will make him run suddenly upon her: and who shall be the chosen one whom I may appoint over her? for who is like to me? and who shall abide me? and who is that shepherd that can withstand my countenance?
20 Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
Therefore hear ye the counsel of the Lord, which he hath taken concerning Edom: and his thoughts which he hath thought concerning the inhabitants of Theman: surely the little ones of the flock shall cast them down, of a truth they shall destroy them with their habitation.
21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
The earth is moved at the noise of their fall: the cry of their voice is heard in the Red Sea.
22 Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
Behold he shall come up as an eagle, and fly: and he shall spread his wings over Bosra: and in that day the heart of the valiant ones of Edom shall be as the heart of a woman in labour.
23 Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
Against Damascus. Emath is confounded and Arphad: for they have heard very bad tidings, they are troubled as in the sea: through care they could not rest.
24 Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
Damascus is undone, she is put to flight, trembling hath seized on her: anguish and sorrows have taken her as a woman in labour.
25 Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
How have they forsaken the city of renown, the city of joy!
26 Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
Therefore her young men shall fall in her streets: and all the men of war shall be silent in that day, saith the Lord of hosts.
27 “Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
And I will kindle a fire in the wall of Damascus, rind it shall devour the strong holds of Benadad.
28 Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
Against Cedar and against the kingdoms of Asor, which Nabuchodonosor king of Babylon destroyed. Thus saith the Lord: Arise, and go ye up to Cedar, and waste the children of the east.
29 Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
They shall take their tents, and their flocks: and shall carry off for themselves their curtains, and all their vessels, and their camels: and they shall call fear upon them round about.
30 “Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
Flee ye, get away speedily, sit in deep holes, you that inhabit Asur, saith the Lord: for Nabuchodonosor king of Babylon hath taken counsel against you, and hath conceived designs against you.
31 “Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
Arise, and so up to a nation that is at ease, and that dwelleth securely, saith the Lord: they have neither gates, nor bars: they dwell alone.
32 Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
And their camels shall be for a spoil, and the multitude of their cattle for a booty, and I will scatter into every wind them that have their hair cut round, and I will bring destruction upon them from I all their confines, saith the Lord.
33 “Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
And Asor shall be a habitation for dragons, desolate for ever: no man shall abide there, nor son of man inhabit it.
34 Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
The word of the Lord that came to Jeremias the prophet against Elam, in the beginning of the reign of Sedecias king of Juda, saying:
35 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
Thus saith the Lord of hosts: Behold I will break the bow of Elam, and their chief strength.
36 Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
And I will bring upon Elam the four winds from the fear quarters of heaven: and I will scatter them into all these winds: and there shall be no nation, to which the fugitives of Elam shall not come.
37 Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
And I will cause Elam to be afraid before their enemies, and in the sight of them that seek their life: and I will bring evil upon them, my fierce wrath, saith the Lord: and will send the sword after them, till I consume them.
38 Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
And I will set my throne in Elam, and destroy kings and princes from thence, saith the Lord.
39 “Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.
But in the latter days I will cause the captives of Elam, to return, saith the Lord.

< Irmiya 49 >