< Irmiya 44 >

1 Wannan maganata zo wa Irmiya game da dukan Yahudawa masu zama a Masar ta Ƙasa, a Migdol, Tafanes da Memfis, da kuma a Masar ta Bisa.
La parole qui fut adressée à Jérémie pour tous les Judéens demeurant dans le pays d'Egypte, demeurant à Migdol, à Taphnès, à Noph et au pays de Phaturès, en ces termes:
2 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa kun ga masifa mai girmar da na kawo a kan Urushalima da kuma a kan dukan garuruwan Yahuda. A yau sun zama hamada da kuma kango
Ainsi parle Yahweh des armées, Dieu d'Israël: Vous avez vu tout le mal que j'ai fait venir sur Jérusalem et sur toutes les villes de Juda: les voilà aujourd'hui dévastées et sans habitants,
3 saboda muguntar da suka aikata. Sun tsokane ni na yi fushi ta wurin ƙone turare da kuma ta wurin bauta wa waɗansu allolin da su ko ku ko kakanninku ba su taɓa sani ba.
à cause du mal qu'ils ont fait pour m'irriter, en allant offrir de l'encens et des hommages à des dieux étrangers qu'ils ne connaissaient pas, ni eux, ni vous, ni vos vos pères.
4 Sau da sau na aiki bayina annabawa, waɗanda suka ce, ‘Kada ku yi wannan abin ƙyama da na ƙi!’
Je vous ai envoyé tous mes serviteurs les prophètes, les envoyant dès le matin, pour vous dire: Ne faites donc pas cette abomination que je hais.
5 Amma ba su saurara ko su kasa kunne ba; ba su juye daga muguntarsu ko su daina ƙone turare wa waɗansu alloli ba.
Mais ils n'ont pas écouté, ils n'ont pas prêté l'oreille pour revenir de leur méchanceté et n'offrir plus d'encens à des dieux étrangers.
6 Saboda haka, fushina mai ƙuna ya fāɗo a kan garuruwan Yahuda da kuma titunan Urushalima na kuma mai da su kufai da suke a yau.
Aussi mon indignation et ma colère ont fondu sur eux et se sont allumées contre les villes de Juda et les rues de Jérusalem, qui sont devenues un lieu dévasté et désert, comme cela se voit aujourd'hui.
7 “To, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa don me kuka kawo irin masifa mai girma haka a kanku ta wurin warewa daga Yahuda maza da mata, yara da jarirai, kun kuma bar kanku babu raguwa?
Et maintenant, ainsi parle Yahweh, Dieu des armées, Dieu d'Israël: Pourquoi vous faites-vous ce grand mal à vous-mêmes, de vous faire exterminer du milieu de Juda, vos hommes et vos femmes, vos enfants et vos nourrissons, sans qu'on vous laisse aucun reste,
8 Me ya sa kuka tsokane ni in yi fushi saboda abin da hannuwanku suka yi, kuna ƙone turare wa waɗansu alloli a Masar, inda kuka zo don ku zauna? Za ku hallakar da kanku ku kuma mai da kanku abin la’ana da abin zargi da abin ba’a a cikin dukan al’umman duniya.
de m'irriter par les œuvres de vos mains, en offrant de l'encens à des dieux étrangers dans le pays d'Egypte, où vous êtes entrés pour y habiter, afin de vous faire exterminer, et afin de devenir un objet de malédiction et d’opprobre parmi tous les peuples de la terre?
9 Kun manta mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakuna da sarauniyoyin Yahuda da mugayen ayyukanku, da na matanku a cikin Yahuda da kan titunan Urushalima?
Avez-vous, oublié les crimes de vos pères, les crimes des rois de Juda, les crimes des femmes de Juda, vos crimes et les crimes de vos femmes, qu'elles ont commis dans le pays de Juda et dans les rues de Jérusalem?
10 Har yă zuwa yau ba su ƙasƙantar da kansu ko su nuna bangirma, ko su kiyaye dokata da ƙa’idodin da na sa a gabanku da kakanninku ba.
Ils n'ont pas été contrits jusqu'à ce jour, ils n'ont pas eu de crainte, ils n'ont pas marché dans ma loi ni dans mes commandements que j'avais mis devant vous et devant vos pères.
11 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa na ƙudura in aukar muku da masifa in kuma hallaka dukan Yahuda.
C'est pourquoi ainsi parle Yahweh des armées, Dieu d'Israël: Voici que je vais tourner ma face contre vous, pour votre malheur, et pour exterminer tout Juda.
12 Zan ɗauke raguwar Yahuda waɗanda suka ƙudurta su je Masar su zauna a can. Duk za su hallaka a Masar; za su mutu ta wurin takobi ko su mutu da yunwa. Daga ƙarami zuwa babba, za su mutu ta wurin takobi ko yunwa. Za su zama abin zarge da abin tsoro, abin la’ana da abin ba’a.
Je prendrai le reste de Juda, qui a tourné ses regards vers le pays d'Egypte pour y venir habiter. Ils seront tous consumés dans le pays d'Egypte et ils tomberont; ils seront consumés par l'épée, par la famine; petits et grands, ils mourront par l'épée et par la famine, et ils seront un objet d'exécration, de stupéfaction, de malédiction et d'opprobre.
13 Zan hukunta waɗanda suke zama a Masar da takobi, yunwa da annoba, yadda na hukunta Urushalima.
Je visiterai ceux qui demeurent dans le pays d'Egypte, comme j'ai visité Jérusalem, par l'épée, par la famine et par la peste.
14 Babu wani daga raguwar Yahuda wanda ya tafi Masar da zai kuɓuta ko ya tsira har ya komo zuwa ƙasar Yahuda, wadda za su yi marmari su komo su zauna; babu wani da zai komo sai dai’yan gudun hijira.”
Nul ne réchappera ni ne survivra du reste de Juda, de ceux qui sont venus pour demeurer ici, au pays d'Egypte, et pour retourner au pays de Juda, où leur désir les pousse à revenir pour y demeurer. Car ils n'y retourneront pas, sauf quelques réchappés.
15 Sai dukan mazan da suka san cewa matansu suna ƙone turare wa waɗansu alloli, tare da dukan matan da suke a nan babban taro, da kuma dukan mutanen da suke zama a Masar ta Ƙasa da ta Bisa, suka ce wa Irmiya,
Alors tous les hommes qui savaient que leurs femmes offraient de l'encens à des dieux étrangers, et toutes les femmes rassemblées là, en grande assemblée, et tout le peuple qui demeurait dans le pays d'Egypte, à Pathurès, répondirent, à Jérémie en ces termes:
16 “Ba za mu saurari saƙon da ka yi mana magana a sunan Ubangiji ba!
" Quant à la parole que tu nous as dite au nom de Yahweh, nous ne t'écoutons pas.
17 Lalle za mu aikata duk abin da muka ce za mu yi. Za mu ƙone turare ga Sarauniyar Sama za mu kuma miƙa hadayun sha gare ta kamar dai yadda mu da kakanninmu, sarakunanmu da fadawanmu muka yi a garuruwan Yahuda da kuma kan titunan Urushalima. A lokacin muna da abinci a yalwace muna kuma da arziki ba mu kuma da wata damuwa.
Mais nous accomplirons certainement toute parole sortie de notre bouche, en offrant de l'encens à la Reine du ciel, en lui versant des libations, comme nous avons fait, nous et nos pères, nos rois et nos chefs, dans les villes de Juda et dans les rues de Jérusalem. Nous avions alors du pain à satiété, nous étions heureux et nous ne voyions pas le malheur.
18 Amma tun da muka daina ƙone turare ga Sarauniyar Sama da kuma miƙa mata hadayun sha, muka rasa kome muna ta mutuwa ta wurin takobi da yunwa.”
Mais depuis que nous avons cessé d'offrir de l'encens à la Reine du ciel et de lui verser des libations, nous avons manqué de tout et nous avons été consumés par l'épée et par la famine.
19 Matan suka ƙara da cewa, “Sa’ad da muka ƙone turare ga Sarauniyar Sama muka kuma miƙa mata hadayun sha, mazanmu ba su san muna yin waina kamar siffarta muna kuma miƙa mata hadayun sha ba?”
Et quand nous offrions de l'encens à la Reine du ciel et que nous lui versions des libations, est-ce en dehors de nos maris que nous lui faisions des gâteaux pour la représenter et que nous lui versions des libations?
20 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutanen, maza da mata, waɗanda suke ba shi amsa,
Alors Jérémie parla à tout le peuple contre les hommes, contre les femmes et contre ceux qui lui avaient ainsi répondu, et il leur dit:
21 “Ubangiji bai tuna ya kuma yi tunani game da turaren da aka ƙone a garuruwan Yahuda da kan titunan Urushalima wanda ku da kakanninku, sarakunanku da fadawanku da mutanen ƙasar ba ne?
" N'est-ce pas l'encens que vous avez brûlé dans les villes de Juda et dans les rues de Jérusalem, vous et vos pères, vos rois et vos chefs, et le peuple du pays, que Yahweh s'est rappelé et qui lui est monté au cœur?
22 Sa’ad da Ubangiji bai iya jurewa da mugayen ayyukanku da kuma abubuwa banƙyama da kuka aikata ba, sai ƙasarku ta zama abin la’ana da kufai babu mazauna yadda yake a yau.
Yahweh n'a pu le supporter plus longtemps, à cause de la méchanceté de vos actions et des abominations que vous avez commises; et votre pays est devenu un lieu désert, dévasté et maudit, où personne n'habite, comme on le voit aujourd'hui.
23 Domin kun ƙone turare kuka kuma yi wa Ubangiji zunubi ba ku kuma yi masa biyayya ko ku kiyaye dokarsa ko ƙa’idodinsa ko farillansa ba, wannan masifa ta aukar muku, yadda yanzu kuka gani.”
C'est parce que vous avez offert de l'encens et péché contre Yahweh et que vous n'avez pas écouté la voix de Yahweh, ses lois, ses ordonnances et ses préceptes, c'est pour cela que ce malheur vous est arrivé, comme cela se voit aujourd'hui. "
24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane, har da mata, “Ku saurari maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda a Masar.
Et Jérémie dit à tout le peuple et à toutes les femmes: " Ecoutez la parole de Yahweh, vous tous, hommes de Juda qui êtes dans le pays d'Egypte.
25 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku da matanku kun nuna ta wurin ayyukanku abin da kuka yi alkawari sa’ad da kuka ce, ‘Lalle za mu yi abin da muka yi alkawari na ƙone turare da kuma miƙa hadayun sha ga Sarauniyar Sama.’ “To, sai ku ci gaba, ku aikata abin da kuka yi alkawari! Ku cika alkawarinku!
Ainsi parle Yahweh des armées, Dieu d'Israël: Vous et vos femmes, vous l'avez déclaré de vos bouches et exécuté de vos mains, en disant: Oui, nous accomplirons les vœux que nous avons faits, d'offrir de l'encens à la Reine du ciel et de lui verser des libations. Eh bien, acquittez vos vœux, ne manquez pas d'accomplir vos vœux!
26 Amma ku ji maganar Ubangiji, dukan Yahudawan da suke zama a Masar, ‘Na rantse da sunana,’ in ji Ubangiji, ‘cewa babu wani daga Yahuda wanda yake zama a ko’ina a Masar zai ƙara kira bisa sunana ko ya rantse ya ce, “Muddin Ubangiji Mai Iko Duka yana raye.”
Ecoutez donc la parole de Yahweh, vous tous, hommes de Juda qui demeurez dans le pays d'Egypte. Voici que je le jure par mon grand nom, dit Yahweh: Mon nom ne sera plus prononcé dans tout le pays d'Egypte par la bouche d'aucun homme de Juda disant: Le Seigneur Yahweh est vivant!
27 Gama ina lura da su don lahani, ba alheri ba; mutanen Yahuda da suke a Masar za su hallaka ta wurin takobi da yunwa sai dukansu sun hallaka.
Voici que je veille sur eux, pour leur mal et non pour leur bien, et tous les hommes de Juda qui sont dans le pays d'Egypte seront consumés par l'épée et par la famine, jusqu'à leur extermination.
28 Waɗanda suka kuɓuta wa takobi suka komo zuwa ƙasar Yahuda daga Masar za su zama kima kawai. Sa’an nan dukan raguwar Yahuda waɗanda suka zo don su yi zama a Masar za su san maganar wane ne za tă tabbata, tawa ko tasu.
Et ceux qui échapperont à l'épée, en petit nombre, retourneront du pays d'Egypte au pays de Juda. Et tout le reste de Juda, ceux qui sont venus en Egypte pour y habiter, sauront de qui la parole sera réalisée, la mienne ou la leur.
29 “‘Wannan zai zama alama a gare ku cewa zan hukunta ku a wannan wuri,’ in ji Ubangiji, ‘saboda ku san cewa barazanata ta lahani a kanku tabbatacce za tă cika.’
Et ceci sera pour vous, — oracle de Yahweh, — le signe que je vous visiterai en ce lieu, afin que vous sachiez que mes paroles s'accompliront certainement pour votre malheur:
30 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Zan bayar da Fir’auna Hofra sarkin Masar ga abokan gābansa waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zedekiya sarkin Yahuda ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, abokin gāban da ya nemi ransa.’”
Ainsi parle Yahweh: Voici que je livre le Pharaon Hophra, roi d'Egypte, aux mains de ses ennemis et aux mains de ceux qui en veulent à sa vie, comme j'ai livré Sédécias, roi de Juda, aux mains de Nabuchodonosor, roi de Babylone, son ennemi, qui en voulait à sa vie. "

< Irmiya 44 >