< Irmiya 43 >

1 Sa’ad da Irmiya ya gama faɗa wa mutane dukan maganar Ubangiji Allahnsu, duk abin da Ubangiji ya aike shi ya faɗa musu,
Und es geschah, als Jirmejahu vollendet hatte zu reden zu allem Volk alle Worte Jehovahs, ihres Gottes, die Jehovah, ihr Gott, an sie durch ihn gesandt hatte, alle diese Worte,
2 Azariya ɗan Hoshahiya da Yohanan ɗan Kareya da dukan masu ɗaga kai suka ce wa Irmiya, “Kana ƙarya ne! Ubangiji Allahnmu bai aike ka ka ce, ‘Kada ku tafi Masar don ku zauna a can.’
Da sprach Asarjah, Hoschajahs Sohn, und Jochanan, Kareachs Sohn, und alle vermessenen Männer, und sprachen zu Jirmejahu: Lüge redest du. Jehovah, unser Gott, hat dich nicht gesandt zu sprechen: Kommt nicht nach Ägypten, als Fremdlinge dort zu weilen;
3 Amma Baruk ɗan Neriya yana zuga ka a kanmu don ka ba da mu ga Babiloniyawa, don su kashe mu ko su kai mu zaman bauta a Babilon.”
Denn Baruch, der Sohn Nerijahs, hat dich angetrieben wider uns, damit er uns in der Chaldäer Hand gebe, daß sie uns töten und uns nach Babel wegführen.
4 Saboda haka Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da dukan mutane suka yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da su zauna a ƙasar Yahuda.
Und Jochanan, Kareachs Sohn, und alle Obersten der Streitmächte und das ganze Volk hörten nicht auf Jehovahs Stimme, daß sie im Lande Jehudah wohnen sollten.
5 A maimako, Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe raguwar Yahuda waɗanda suka dawo su zauna a ƙasar Yahuda daga dukan al’umman inda aka kora su.
Und Jochanan, der Sohn Kareachs, und alle Obersten der Streitmächte nahmen allen Überrest von Jehudah, die, so von allen Völkerschaften, dahin sie verstoßen worden, zurückgekommen waren, um im Lande Jehudah zu weilen,
6 Suka kuma kwashe dukan maza, mata da yara da’ya’yan sarki mata waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari tare da Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da Irmiya annabi da kuma Baruk ɗan Neriya.
Die Männer und die Weiber und die Kindlein und die Töchter des Königs und jede Seele, die Nebusaradan, der Hauptmann der Leibwachen bei Gedaljahu, dem Sohne Achikams, des Sohnes von Schaphan, und bei Jirmejahu, dem Propheten, und bei Baruch, Nerijahs Sohn, gelassen hatte,
7 Saboda haka suka shiga Masar cikin rashin biyayya ga Ubangiji suka tafi har can Tafanes.
Und sie gingen ein in das Land Ägypten, weil sie nicht auf die Stimme Jehovahs hörten, und kamen bis Thachpanches.
8 A Tafanes maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Und es geschah das Wort Jehovahs an Jirmejahu in Thachpanches, sprechend:
9 “Yayinda Yahudawa suna kallo, ka ɗauki waɗansu manyan duwatsu tare da kai ka kuma binne su cikin yumɓu a tubalin dakalin ƙofar shiga fadar Fir’auna a Tafanes.
Nimm in deine Hand große Steine und lege sie hehlings in den Lehm im Ziegelofen an den Eingang in das Haus Pharos, in Thachpanches vor den Augen der jüdischen Männer,
10 Sa’an nan ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, zan aika wa bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon, zan kuma sa kursiyinsa a kan waɗannan duwatsun da na binne a nan; zai fadada bukkar mulkinsa a bisansu.
Und sprich zu ihnen: Also spricht Jehovah der Heerscharen, der Gott Israels: Siehe, Ich sende und hole Nebuchadrezzar, Babels König, meinen Knecht, und setze seinen Thron über diese Steine, die Ich hehlings hingelegt habe, und er spanne sein Gezelt aus über sie.
11 Zai zo ya yaƙi Masar, ya kawo mutuwa ga waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa, zaman bauta ga waɗanda aka ƙaddara musu zaman bauta, da kuma takobi ga waɗanda aka ƙaddara su mutu ta takobi.
Und er kommt und schlägt das Land Ägypten: mit dem Tode die, so des Todes sind, mit Gefangenschaft die, so für Gefangenschaft sind, mit dem Schwert, die für das Schwert sind.
12 Zai sa wuta wa haikalan allolin Masar; zai ƙone haikalansu yă kuma kwashe allolinsu bayi. Kamar yadda makiyayi yakan yafa mayafinsa kewaye da shi, haka zai yafa Masar kewaye da kansa ya kuma tashi a wurin babu abin da ya same shi.
Und Feuer zünde Ich an in den Häusern der Götter Ägyptens, daß er sie verbrenne, und sie gefangen führe und sich umhülle mit dem Lande Ägypten, wie der Hirt sich mit seinem Kleid umhüllt und geht aus davon im Frieden.
13 A can cikin haikalin rana a Masar zai rushe al’amudan duwatsu yă kuma ƙone haikalan allolin Masar.’”
Und soll die Bildsäulen des Sonnenhauses im Lande Ägypten zerbrechen und die Häuser der Götter Ägyptens mit Feuer verbrennen.

< Irmiya 43 >