< Irmiya 29 >

1 Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
Now these are the words of the letter that Jeremiah the prophet sent from Jerusalem to the residue of the elders of the captivity, and to the priests, to the prophets, and to all the people, whom Nebuchadnezzar had carried away captive from Jerusalem to Babylon,
2 (Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
(after that Jeconiah the king, the queen mother, the eunuchs, the officials of Judah and Jerusalem, the craftsmen, and the metal workers, had departed from Jerusalem),
3 Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
by the hand of Elasah the son of Shaphan, and Gemariah the son of Hilkiah, (whom Zedekiah king of Judah sent to Babylon to Nebuchadnezzar king of Babylon), saying,
4 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
"Thus says Jehovah of hosts, the God of Israel, to all the captivity, whom I have caused to be carried away captive from Jerusalem to Babylon:
5 “Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
'Build houses, and dwell in them; and plant gardens, and eat their fruit.
6 Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
Take wives, and father sons and daughters; and take wives for your sons, and give your daughters to husbands, that they may bear sons and daughters; and multiply there, and do not be diminished.
7 Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
Seek the peace of the city where I have caused you to be carried away captive, and pray to Jehovah for it; for in its peace you shall have peace.'
8 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
For thus says Jehovah of hosts, the God of Israel: 'Do not let your prophets who are in the midst of you, and your diviners, deceive you; neither listen to your dreams which you cause to be dreamed.
9 Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
For they prophesy falsely to you in my name: I have not sent them,' says Jehovah.
10 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
"For thus says Jehovah, 'After seventy years are accomplished for Babylon, I will visit you, and perform my good word toward you, in causing you to return to this place.
11 Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
For I know the plans that I have for you,' says Jehovah, 'plans for your welfare, and not for calamity, to give you hope and a future.
12 Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
You shall call on me, and you shall go and pray to me, and I will listen to you.
13 Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
You shall seek me, and find me, when you shall search for me with all your heart.
14 Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
I will be found by you,' says Jehovah, 'and I will turn again your captivity, and I will gather you from all the nations, and from all the places where I have driven you,' says Jehovah; 'and I will bring you again to the place from where I caused you to be carried away captive.'
15 Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
"Because you have said, 'Jehovah has raised us up prophets in Babylon';
16 Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
thus says Jehovah concerning the king who sits on the throne of David, and concerning all the people who dwell in this city, your brothers who haven't gone forth with you into captivity;
17 I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
thus says Jehovah of hosts; 'Look, I will send on them the sword, the famine, and the pestilence, and will make them like vile figs, that can't be eaten, they are so bad.
18 Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
I will pursue after them with the sword, with the famine, and with the pestilence, and will deliver them to be tossed back and forth among all the kingdoms of the earth, to be an object of horror, and an astonishment, and a hissing, and a reproach, among all the nations where I have driven them;
19 Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
because they have not listened to my words,' says Jehovah, 'with which I sent to them my servants the prophets, rising up early and sending them; but you would not hear,' says Jehovah.
20 Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
'Hear therefore the word of Jehovah, all you of the captivity, whom I have sent away from Jerusalem to Babylon.'
21 Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
"Thus says Jehovah of hosts, the God of Israel, concerning Ahiab the son of Kolaiah, and concerning Zedekiah the son of Maaseiah, who prophesy a lie to you in my name: 'Look, I will deliver them into the hand of Nebuchadnezzar king of Babylon; and he shall kill them before your eyes;
22 Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
and of them shall be taken up a curse by all the captives of Judah who are in Babylon, saying, "Jehovah make you like Zedekiah and like Ahiab, whom the king of Babylon roasted in the fire";
23 Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
because they have worked folly in Israel, and have committed adultery with their neighbors' wives, and have spoken words in my name falsely, which I did not command them; and I am he who knows, and am witness,' says Jehovah."
24 Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
"Concerning Shemaiah the Nehelamite you shall speak, saying,
25 “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
'Thus speaks Jehovah of hosts, the God of Israel, saying, "Because you have sent letters in your own name to all the people who are at Jerusalem, and to Zephaniah the son of Maaseiah, the priest, and to all the priests, saying,
26 ‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
'Jehovah has made you priest in the place of Jehoiada the priest, that there may be officers in the house of Jehovah, for every man who is mad, and makes himself a prophet, that you should put him in the stocks and in shackles.
27 To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
Now therefore, why have you not rebuked Jeremiah of Anathoth, who makes himself a prophet to you,
28 Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
because he has sent to us in Babylon, saying, "The captivity is long: build houses, and dwell in them; and plant gardens, and eat their fruit?"'"'
29 Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
Zephaniah the priest read this letter in the ears of Jeremiah the prophet.
30 Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
Then came the word of Jehovah to Jeremiah, saying,
31 “Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
"Send to all them of the captivity, saying, 'Thus says Jehovah concerning Shemaiah the Nehelamite: "Because Shemaiah has prophesied to you, and I did not send him, and he has caused you to trust in a lie;
32 ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”
therefore," thus says Jehovah, "Look, I will punish Shemaiah the Nehelamite, and his offspring; he shall not have a man to dwell among this people, neither shall he see the good that I will do to my people, says Jehovah, because he has spoken rebellion against Jehovah."'"

< Irmiya 29 >