< Irmiya 17 >

1 “An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
The synne of Juda is writun with an irone poyntel, in a nail of adamaunt; it is writun on the breede of the herte of hem, and in the hornes of the auteris of hem.
2 Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
Whanne the sones of hem bithenken on her auteris, and woodis, and on the trees ful of boowis, makynge sacrifice in the feld in hiye munteyns,
3 Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
Y schal yyue thi strengthe and alle thi tresouris in to rauyschyng, thin hiye thingis for synnes in alle thin endis.
4 Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
And thou schalt be left aloone fro thin eritage which Y yaf to thee; and Y schal make thee to serue thin enemyes, in the lond which thou knowist not; for thou hast kyndlid fier in my strong veniaunce, it schal brenne til in to with outen ende.
5 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
The Lord seith these thingis, Cursid is the man that trestith in man, and settith fleisch his arm, and his herte goith awei fro the Lord.
6 Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
For he schal be as bromes in desert, and he schal not se, whanne good schal come; but he schal dwelle in drynesse in desert, in the lond of saltnesse, and vnabitable.
7 “Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
Blessid is the man that tristith in the Lord, and the Lord schal be his trist.
8 Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
And he schal be as a tre, which is plauntid ouer watris, which sendith hise rootis to moisture; and it schal not drede, whanne heete schal come; and the leef therof schal be greene, and it schal not be moued in the tyme of drynesse, nether ony tyme it schal faile to make fruyte.
9 Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
The herte of man is schrewid, and `may not be souyt; who schal knowe it?
10 “Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
Y am the Lord sekynge the herte, and preuynge the reynes, and Y yyue to ech man after his weye, and aftir the fruyt of his fyndyngis.
11 Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
A partriche nurschide tho thingis whiche sche bredde not; he made richessis, and not in doom; in the myddis of hise daies he schal forsake tho, and in hise laste tyme he schal be vnwijs.
12 Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
The seete of glorie of hiynesse was at the bigynnyng the place of oure halewyng, the abidyng of Israel.
13 Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
Lord, alle thei that forsaken thee, schulen be schent; thei that goen aweie fro thee, schulen be writun in erthe, for thei han forsake the Lord, a veyne of quyk watirs.
14 Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
Lord, heele thou me, and Y schal be heelid; make thou me saaf, and Y schal be saaf; for thou art myn heriyng.
15 Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
Lo! thei seien to me, Where is the word of the Lord? come it.
16 Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
And Y am not disturblid, suynge thee scheepherd, and Y desiride not the dai of man, thou woost. That that yede out of my lippis was riytful in thi siyt.
17 Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
Be thou not to drede to me; thou art myn hope in the dai of turment.
18 Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
Be thei schent, that pursuen me, and be Y not schent; drede thei, and drede not Y; brynge in on hem a dai of turment, and defoule thou hem bi double defouling.
19 Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
The Lord seith these thingis to me, Go thou, and stonde in the yate of the sones of the puple, bi whiche the kingis of Juda entren and goen out, and in alle the yatis of Jerusalem.
20 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
And thou schalt seie to hem, Here the word of the Lord, ye kingis of Juda, and al Judee, and alle the dwelleris of Jerusalem, that entren bi these yatis.
21 Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
The Lord God seith these thingis, Kepe ye youre soulis, and nyle ye bere birthuns in the dai of sabat, nether bringe in bi the yatis of Jerusalem.
22 Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
And nyle ye caste birthuns out of youre housis in the dai of sabat, and ye schulen not do ony werk; halewe ye the dai of sabat, as Y comaundide to youre fadris.
23 Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
And thei herden not, nether bowiden doun her eere, but thei maden hard her nol, that thei schulden not here me, and that thei schulden not take chastisyng.
24 Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
And it schal be, if ye heren me, seith the Lord, that ye bere not in birthuns bi the yatis of this citee in the dai of sabat, and if ye halewen the dai of sabat, that ye do not werk ther ynne,
25 sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
kingis and princes sittynge on the seete of Dauid schulen entre bi the yatis of this citee, and stiynge in charis and horsis; thei, and the princis of hem, the men of Juda, and the dwelleris of Jerusalem; and this citee schal be enhabitid withouten ende.
26 Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
And thei schulen come fro the citees of Juda, and fro the cumpas of Jerusalem, and fro the lond of Beniamyn, and fro feeldi places, and fro hilli places, and fro the south, beringe brent sacrifice, and slayn sacrifice, and encense; and thei schulen bringe offring in to the hous of the Lord.
27 Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”
Forsothe if ye heren not me, that ye halewe the dai of sabat, and that ye bere not a birthun, and that ye bringe not in bi the yatis of Jerusalem in the dai of sabat, Y schal kyndle fier in the yatis therof; and it schal deuoure the housis of Jerusalem, and it schal not be quenchid.

< Irmiya 17 >