< Irmiya 16 >

1 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Potom doðe mi rijeè Gospodnja govoreæi:
2 “Kada ka yi aure ka haifi’ya’ya maza da mata a wannan wuri.”
Nemoj se ženiti, i da nemaš sinova ni kæeri na tom mjestu.
3 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da’ya’ya maza da matan da aka haifa a wannan ƙasa da kuma game da matan da suke iyayensu da suke mazan da iyayensu.
Jer ovako govori Gospod za sinove i kæeri što se rode na tom mjestu i za matere njihove koje ih rode, i za oce njihove koji ih rode u toj zemlji:
4 “Za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi kuka dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba, amma za a bar su a juji. Takobi da yunwa ne za su hallaka su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da kuma namun jeji na duniya.”
Ljutom æe smræu pomrijeti, neæe biti oplakani niti æe se pogrepsti, biæe gnoj po zemlji, i od maèa i od gladi izginuæe, i mrtva æe tjelesa njihova biti hrana pticama nebeskim i zvijerima zemaljskim.
5 Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ka shiga gidan da akwai abincin makoki; kada ka tafi ka yi makoki ko ka nuna juyayi, domin na janye albarkata, ƙaunata da tausayina daga wannan mutane,” in ji Ubangiji.
Jer ovako govori Gospod: ne ulazi u kuæu u kojoj je žalost, i ne idi da plaèeš niti ih žali; jer sam uzeo mir svoj od toga naroda, govori Gospod, milost i žaljenje.
6 “Manya da ƙanana duka za su mutu a wannan ƙasa. Ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi makokinsu ba, kuma ba wanda zai tsaga kansa ko ya aske kansa saboda su.
Pomrijeæe mali i veliki u ovoj zemlji, neæe biti pogrebeni niti æe se oplakati, niti æe se ko rezati ni glave striæi za njima.
7 Ba wanda zai ba da abinci don yă ta’azantar da waɗanda suke makoki saboda matattu, kai, ko saboda mahaifi ko mahaifiya ma ba kuwa wani da zai ba da abin sha don yă ta’azantar da su.
Neæe im se dati hljeba u žalosti da se potješe za mrtvijem, niti æe ih napojiti iz èaše radi utjehe za ocem ili za materom.
8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki ka zauna don ci da sha.
Tako ne ulazi u kuæu u kojoj je žalost da sjedeš s njima da jedeš i piješ.
9 Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa a idanunka da kuma a kwanakinka zan kawo ƙarshen muryar farin ciki da murna da kuma muryoyin amarya da ango a wannan wuri.
Jer ovako veli Gospod nad vojskama Bog Izrailjev: evo, ja æu uèiniti da na ovom mjestu pred vašim oèima i za vaših dana ne bude glasa radosna ni glasa vesela, glasa ženikova ni glasa nevjestina.
10 “Sa’ad da ka faɗa wa waɗannan mutane wannan duka suka kuma tambaye ka, ‘Me ya sa Ubangiji ya ƙaddara irin wannan babban masifa a kanmu? Wace mugunta muka yi? Wane zunubi muka aikata wa Ubangiji Allahnmu?’
A kad kažeš tome narodu sve ove rijeèi, ako ti reku: zašto izreèe Gospod sve to veliko zlo na nas? i kako je bezakonje naše ili kaki je grijeh naš, kojim zgriješismo Gospodu Bogu svojemu?
11 Sai ka ce musu, ‘Wannan ya zama haka domin kakanninku sun rabu da ni,’ in ji Ubangiji, ‘suka bi waɗansu alloli suka kuma bauta musu. Suka rabu da ni, ba su kuwa kiyaye dokata ba.
Tada im reci: jer oci vaši ostaviše mene, govori Gospod, i idoše za drugim bogovima i služiše im i klanjaše im se, a mene ostaviše i zakona mojega ne držaše;
12 Amma kun yi laifi fiye da kakanninku. Duba yadda kowannenku yana bin taurin muguwar zuciyarsa a maimakon yin mini biyayya.
A vi još gore èinite nego oci vaši, jer eto idete svaki po misli srca svojega zloga ne slušajuæi mene.
13 Saboda haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasar da ku da kakanninku ba ku taɓa sani ba, a can kuwa za ku bauta wa waɗansu alloli dare da rana, gama ba zan nuna muku tagomashi ba.’
Zato æu vas izbaciti iz ove zemlje u zemlju koje ne poznaste ni vi ni oci vaši, i ondje æete služiti drugim bogovima dan i noæ dokle vam ne uèinim milost.
14 “Amma fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga Masar,’
Zato, evo, idu dani, govori Gospod, kad se neæe više govoriti: tako da je živ Gospod koji je izveo sinove Izrailjeve iz zemlje Misirske;
15 amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fitar da Isra’ilawa daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su.’ Gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba wa kakanninsu.
Nego: tako da je živ Gospod koji je izveo sinove Izrailjeve iz zemlje sjeverne i iz svijeh zemalja u koje ih bješe razagnao! Jer æu ih opet dovesti u zemlju njihovu koju sam dao ocima njihovijem.
16 “Amma yanzu zan aiko a kira masunta masu yawa su zo,” in ji Ubangiji, “za su kuma kama su. Bayan wannan zan aiko a kira mafarauta su zo, su farauce su daga kowane dutse da tudu da kuma daga kogwannin duwatsu.
Gle, ja æu poslati mnoge ribare, govori Gospod, da ih love, i poslije æu poslati mnoge lovce da ih love po svakoj gori i po svakom humu i po rasjelinama kamenijem.
17 Idanuna suna a kan dukan hanyoyinsu; ba a ɓoye suke daga gare ni, kuma zunubansu ba a ɓoye suke a idanuna ba.
Jer oèi moje paze na sve putove njihove, nijesu sakriveni od mene, niti je bezakonje njihovo zaklonjeno od mojih oèiju.
18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, suka kuma cika abin gādona da gumakansu na banƙyama.”
I platiæu im prvo dvojinom za bezakonje njihovo i za grijeh njihov, što oskvrniše zemlju moju strvima gadova svojih, i našljedstvo moje napuniše gnusobama svojim.
19 Ya Ubangiji, ƙarfina da katangana, mafakata a lokacin damuwa, gare ka al’ummai za su zo daga iyakokin duniya su ce, “Kakanninmu ba su mallaki kome ba sai allolin ƙarya, gumakan banza da ba su yi musu amfani ba.
Gospode, krjeposti moja i grade moj i utoèište moje u nevolji, k tebi æe doæi narodi od krajeva zemaljskih, i reæi æe: doista oci naši imaše laž, i taštinu i što nimalo ne pomaže.
20 Mutane kan yi allolinsu ne? I, amma waɗannan ba alloli ba ne!”
Eda li æe èovjek naèiniti sebi bogove, koji ipak nijesu bogovi?
21 “Saboda haka zan koya musu a wannan lokaci zan koya musu ikona da ƙarfina. Sa’an nan za su sani cewa sunana Ubangiji ne.
Zato, evo, ja æu ih nauèiti sada, pokazaæu im ruku svoju i silu svoju, da poznadu da mi je ime Gospod.

< Irmiya 16 >