< Irmiya 10 >

1 Ku ji abin da Ubangiji yana ce muku, ya gidan Isra’ila.
Hörer hvad Herren säger till eder, I af Israels hus.
2 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kada ku koyi hanyoyin al’ummai ko ku razana game da alamun sararin sama, ko da yake al’ummai sun razana saboda su.
Detta säger Herren: I skolen icke lära Hedningarnas sätt, och skolen intet frukta eder för himmelens tecken, såsom Hedningarna frukta.
3 Gama al’adun mutane banza ne; sukan yanke itace daga kurmi, sai mai sassaƙa yă sassaƙa shi da gizago.
Ty Hedningarnas gudar äro icke utan fåfängelighet; de hugga ett trä i skogenom, och mästaren gör det till med en yxa;
4 Sukan yi masa ado da azurfa da kuma zinariya; sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, don kada yă fāɗi.
Och pryder det med silf och guld, och fäster det vid, med naglar och hamrar, att det icke omkullfalla skall.
5 Kamar dodon gona cikin gonar kabewa, haka gumakansu ba sa iya magana; dole a yi ta ɗaukansu domin ba za su iya tafiya ba. Kada ku ji tsoronsu; ba za su iya yi wa wani lahani ba ba sa iya yin wani abin kirki.”
Sådant är nu intet annat, än öfverdragna stodar; de kunna intet tala; så måste man ock bära dem; ty de kunna intet gå. Derföre skolen I intet frukta eder för dem; förty de kunna hvarken hjelpa eller stjelpa.
6 Babu wani kamar ka, ya Ubangiji; kai mai girma ne, kuma sunanka yana da girma da kuma iko.
Men dig, Herre, är ingen lik; du äst stor, och ditt Namn är stort, och du kan det bevisa med gerningarna.
7 Wane ne ba zai girmama ka ba, Ya Sarkin al’ummai? Tsoronka wajibi ne. A cikin dukan masu hikima na al’ummai kuma cikin dukan mulkokinsu, babu kamar ka.
Ho skulle icke frukta dig, du Hedningarnas Konung? Dig skall man ju lyda; ty ibland alla Hedningarnas visa, och i all Konungarike, är ingen din like.
8 Dukansu marasa azanci ne wawaye; gumakan itacen banza ne suke koya musu.
De äro allesamman dårar och galne; ty ett trä måste ju vara en platt fåfäng Gudstjenst.
9 An kawo ƙeraren azurfa daga Tarshish zinariya kuma daga Ufaz. Abin da gwani da maƙerin zinariya suka yi sa’an nan aka yi masa ado da mulufi da shunayya dukan aikin gwanaye.
Silfskifvor förer man till på hafvet; guld ifrån Uphas, af mästare och guldsmeder beredt; gult silke och purpur kläder man uppå dem, och äro alltsammans slöga, mäns verk.
10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya; shi ne Allah mai rai, madawwamin sarki. Sa’ad da ya yi fushi, ƙasa takan girgiza; al’ummai ba sa iya jure da hasalarsa.
Men Herren är en rätt Gud, en lefvandes Gud, en evig Konung; för hans vrede bäfvar jorden, och Hedningarna kunna icke fördraga hans trug.
11 “Ka faɗa musu wannan, ‘Waɗannan alloli, waɗanda ba su yi sammai da ƙasa ba, za su hallaka daga duniya da kuma daga ƙarƙashin sammai.’”
Så säger nu alltså till dem: De gudar, som himmel och jord icke gjort hafva, förgånge af jorden, och under himmelen.
12 Amma Allah ya yi duniya ta wurin ikonsa; ya kafa duniya ta wurin hikimarsa ya shimfiɗa sammai ta wurin fahiminsa.
Men han hafver gjort jordena genom sina kraft, och verldenes krets beredt genom sina vishet; och utsträckt himmelen genom sitt förstånd.
13 Sa’ad da ya yi tsawa, ruwaye a cikin sammai sukan yi ƙugi; yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya. Yakan aiki walƙiya da ruwan sama ya fitar da iska daga gidajen ajiyarsa.
Då han dundrar, så är mycket vatten under himmelen, och drager upp dimbona ifrå jordenes anda; han gör ljungelden i regnet, och låter vädret kommer ifrå hemlig rum.
14 Kowa marar azanci ne, marar ilimi; kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa. Siffofinsa ƙarya ne; ba su da numfashi a cikinsu.
Alla menniskor äro dårar med sine konst, och alle guldsmeder stå med skam med sin beläte; ty deras beläte äro bedrägeri, och hafva intet lif.
15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne; Sa’ad da hukuncinsu ya yi za su lalace.
Det är alltsammans ett fåfängt och bedrägeligit verk; de måste förgås, då de hemsökte varda.
16 Shi da yake Rabon Yaƙub ba kamar waɗannan yake ba, gama shi ne Mahaliccin abubuwa duka, har da Isra’ila, kabilar gādonsa Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
Men sådan är icke han, som Jacobs lott är; utan han är den som all ting skapat hafver, och Israel är hans arfvedel; han heter Herren Zebaoth.
17 Ku tattara kayayyakinku don ku bar ƙasar, ku da kuke zaune a wurin da aka kewaye da yaƙi.
Tag din handel bort utu landena, du som bor i den fasta ( staden ).
18 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan lokaci zan jefar da waɗanda suke zaune a ƙasar; zan kawo damuwa a kansu domin a kama su.”
Ty så säger Herren: Si, jag skall i denna resone bortslunga landsens inbyggare, och så plåga dem, att de det känna skola.
19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini! Raunina ba mai warkewa ba ne! Duk da haka na ce wa kaina, “Wannan ciwona ne, dole kuma in jure da shi.”
Ack! min jämmer och hjertans sorg; men jag tänker, att det är min plåga; jag måste lida henne.
20 An lalatar da tentina; dukan igiyoyinsa sun tsintsinke.’Ya’yana maza sun bar ni ba sa nan; ba wanda aka bari da zai kafa tentina ko ya kafa mini mafaka.
Mitt tjäll är förstördt, och all min tåg äro sönder; min barn äro borto, och icke mer för handene; ingen upprättar min hyddo igen, och mitt tjäll slår ingen upp igen.
21 Makiyaya marasa azanci ne kuma ba sa neman nufin Ubangiji; saboda haka ba sa nasara dukan garkensu kuwa ya watse.
Ty herdarna äro till dårar vordne, och fråga intet efter Herran; derföre kunna de ock intet rätt lära, utan förskingra hjorden.
22 Ku saurara! Rahoto yana zuwa babban hargitsi daga ƙasar arewa! Zai mai da garuruwan Yahuda kufai, mazaunin diloli.
Si, ett rykte kommer, och ett stort bäfvande af det landet norrut, att Juda städer skola ödeläggas, och till drakaboningar varda.
23 Na sani, ya Ubangiji, cewa ran mutum ba nasa ba ne; ba mutum ne yake kiyaye takawarsa ba.
Jag vet, Herre, att menniskones väg står icke till henne; och det står i ingens mans magt, huru han vandra eller sin gång styra skall.
24 Ka yi mini gyara, Ubangiji, amma fa da adalci kaɗai ba cikin fushinka ba, don kada ka wofinta ni.
Näps mig, Herre, dock med måttelighet, och icke uti dine grymhet; på det du icke skall platt göra mig till intet.
25 Ka zuba hasalarka a kan al’umman da ba su san ka ba, a kan mutanen da ba sa kira bisa sunanka. Gama sun cinye Yaƙub; sun cinye shi gaba ɗaya suka kuma lalace wurin zamansa.
Men gjut dina vrede ut öfver Hedningarna som intet känna dig, och öfver de slägte som intet åkalla ditt Namn: ty de hafva uppfrätit och uppsvulgit Jacob; de hafva gjort en ända med honom, och hans boning förödt.

< Irmiya 10 >