< Ishaya 66 >

1 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sama kursiyina ce, duniya kuma matashin sawuna. Ina gidan da za ku gina mini? Ina wurin hutuna zai kasance?
This is what Yahweh says, “Heaven is my throne, and the earth is my footstool. Where then is the house you will build for me? Where is the place where I may rest?
2 Ba hannuna ba ne ya yi dukan waɗannan abubuwa, ta haka suka kasance?” In ji Ubangiji. “Wannan mutum ne nake jin daɗi, shi da yake mai ƙasƙanci da kuma zuciyar yin tuba, yana kuma rawar jiki ga maganata.
My hand has made all these things; that is how these things came to be—this is Yahweh's declaration. This is the man of whom I approve, the broken and contrite in spirit, and who trembles at my word.
3 Amma duk ya miƙa hadayar bijimi yana kama da wanda ya kashe mutum, kuma duk wanda ya miƙa ɗan rago, kamar wanda ya karye wuyan kare; duk wanda ya miƙa hadaya ta gari yana kama da wanda ya yi sadakar jinin alade, kuma duk wanda ya ƙone turaren tuni, kamar wanda yake bauta gunki ne. Sun zaɓi hanyoyinsu, rayukansu kuma suna jin daɗin abubuwan banƙyamarsu;
He who slaughters an ox also murders a man; he who sacrifices a lamb also breaks a dog's neck; he who offers a grain offering offers swine's blood; he who offers a memorial of incense also blesses wickedness. They have chosen their own ways, and they take pleasure in their abominations.
4 saboda haka ni ma zan aukar musu da masifa mai zafi in kuma kawo musu abin da suke tsoro. Gama sa’ad da na yi kira, ba wanda ya amsa, sa’ad da na yi magana, ba wanda ya saurara, Sun aikata mugunta a idona suka kuma zaɓa abin da ba na jin daɗi.”
In the same way I will choose their own punishment; I will bring on them what they fear, because when I called, no one answered; when I spoke, no one listened. They did what was evil in my sight, and chose to do what displeases me.”
5 Ku ji maganar Ubangiji, ku da kuke rawar jiki ga maganarsa, “’Yan’uwanku da suke ƙinku, suna kuma ware ku saboda sunana, sun ce, ‘Bari a ɗaukaka Ubangiji, don mu ga farin cikinku!’ Duk da haka za su sha kunya.
Hear the word of Yahweh, you who tremble at his word, “Your brothers who hate and exclude you for my name's sake have said, 'May Yahweh be glorified, then we will see your joy,' but they will be put to shame.
6 Ku ji wannan hayaniya daga birni, ku ji surutu daga haikali! Amon Ubangiji ne yana sāka wa abokan gābansa abin da ya dace da su.
A sound of battle tumult comes from the city, a sound from the temple, the sound of Yahweh paying back his enemies.
7 “Kafin naƙuda ya fara mata, ta haihu; kafin zafi ya zo mata, ta haifi ɗa.
Before she goes into labor, she gives birth; before pain is upon her, she gave birth to a son.
8 Wa ya taɓa jin irin wannan abu? Wa ya taɓa gani irin abubuwan nan? Za a iya ƙirƙiro ƙasa a rana ɗaya ko a haifi al’umma farat ɗaya? Duk da haka da zarar Sihiyona ta fara naƙuda sai ta haifi’ya’yanta.
Who has heard of such a thing? Who has seen such things? Will a land be born in one day? Can a nation be established in one moment? Yet as soon as Zion goes into labor, she gives birth to her children.
9 Zan kai mace har haihuwa in kuma sa ta kāsa haihu?” In ji Ubangiji. “Zan rufe mahaihuwa sa’ad da lokacin haihuwa ya yi?” In ji Allahnku.
Do I bring a baby to the birth opening and not permit the child to be born?—asks Yahweh. Or do I bring a child to moment of delivery and then hold it back?—asks your God.”
10 “Ku yi farin ciki tare da Urushalima ku kuma yi murna saboda ita, dukanku waɗanda kuke ƙaunarta; ku yi farin ciki matuƙa tare da ita, dukanku waɗanda kuke makoki a kanta.
Rejoice with Jerusalem and be glad for her, all you who love her; rejoice with her, all you who mourned over her!
11 Gama za ku tsotsa ku kuma ƙoshi da nonon ta’aziyyarta; za ku sha sosai ku kuma ji daɗin yalwarta.”
For you will nurse and be satisfied; with her breasts you will be comforted; for you will drink them to the full and be delighted with the abundance of her glory.
12 Gama ga abin da Ubangiji ya faɗa, “Zan fadada salama gare ta kamar kogi, wadatar al’ummai kuma kamar rafi mai gudu; za ku tsotsa a kuma riƙe ku a hannunta ku kuma yi wasa a gwiwoyinta.
This is what Yahweh says, “I am about to spread prosperity over her like a river, and the riches of the nations like an overflowing stream. You will nurse at her side, be carried in her arms, and be dandled on her knees.
13 Kamar yadda uwa takan ta’azantar da ɗanta haka zan ta’azantar da ku; za ku kuma ta’azantu a Urushalima.”
As a mother comforts her child, so I will comfort you, and you will be comforted in Jerusalem.”
14 Sa’ad da kuka ga wannan, zuciyarku za tă yi farin ciki za ku kuma haɓaka kamar ciyawa; za a sanar da hannun Ubangiji ga bayinsa, amma za a nuna wa maƙiyansa fushinsa.
You will see this, and your heart will rejoice, and your bones will sprout like the tender grass. The hand of Yahweh will be made known to his servants, but he will show his anger against his enemies.
15 Ga shi, Ubangiji yana zuwa da wuta, kuma kekunan yaƙinsa suna kama da guguwa; zai sauko da fushinsa da zafi, tsawatawarsa kuma da harsunan wuta.
For look, Yahweh is coming with fire, and his chariots are coming like the windstorm to bring the heat of his anger and his rebuke with flames of fire.
16 Gama da wuta da kuma takobi Ubangiji zai yi hukunci a kan dukan mutane, kuma yawanci za su kasance waɗanda Ubangiji zai kashe.
For Yahweh executes judgment on mankind by fire and with his sword. Those killed by Yahweh will be many.
17 “Waɗanda suka tsarkake suka kuma tsabtacce kansu don su je lambu, suna bin wannan da yake tsakiya waɗannan da suke cin naman aladu da ɓeraye da waɗansu abubuwan banƙyama, za su sadu da ƙarshensu tare,” in ji Ubangiji.
They consecrate themselves and make themselves pure, so they may enter the gardens, following the one in the middle of those who eat the flesh of pig and abominable things like mice. “They will come to an end—this is Yahweh's declaration.
18 “Ni kuwa, saboda ayyukansu da kuma tunaninsu, ina dab da zuwa in tattara dukan al’ummai da harsuna, za su kuma zo su ga ɗaukakata.
For I know their deeds and their thoughts. The time is coming when I will gather all nations and languages. They will come and will see my glory.
19 “Zan kafa alama a cikinsu, zan kuma aika waɗansu da suka tsira zuwa al’ummai, zuwa Tarshish, zuwa Libiya da Lidiya (sanannun’yan aika), zuwa Tubal da kuma Girka, da kuma zuwa manisantan tsibirai da ba su taɓa jin labarin sunana ba ko su ga ɗaukakata. Za su yi shelar ɗaukakata a cikin al’ummai.
I will set a mighty sign among them. Then I will send survivors from them to the nations: To Tarshish, Put, and Lud, archers who draw their bows, to Tubal, Javan, and to the distant coastlands where they have not heard about me nor seen my glory. They will proclaim my glory among the nations.
20 Za su kuma dawo da dukan’yan’uwanku, daga dukan al’ummai, zuwa dutsena mai tsarki a Urushalima kamar hadaya ga Ubangiji, a kan dawakai, a kekunan yaƙi da wagonu, da kuma a kan alfadarai da kuma raƙuma,” in ji Ubangiji. “Za su kawo su, kamar yadda Isra’ilawa suke kawo hadayun hatsi, zuwa haikalin Ubangiji a cikin tsabtatattun kore.
They will bring back all your brothers out of all the nations, as an offering to Yahweh. They will come on horses, and in chariots, in wagons, on mules, and on camels, to my holy mountain Jerusalem—says Yahweh. For the people of Israel will bring a grain offering in a clean vessel into the house of Yahweh.
21 Zan kuwa zaɓa waɗansunsu kuma su zama firistoci da Lawiyawa,” in ji Ubangiji.
Some of these I will even choose as priests and Levites—says Yahweh.
22 “Kamar yadda sabuwar duniya da sabuwar sama za su tabbata a gabana,” in ji Ubangiji, “haka sunanku da zuriyarku za su tabbata.
For just as the new heavens and the new earth that I will make will remain before me—this is Yahweh's declaration—so your descendants will remain, and your name will remain.
23 Daga wannan sabon wata zuwa wancan, kuma daga wannan Asabbaci zuwa wancan, dukan mutane za su zo su rusuna a gabana,” in ji Ubangiji.
From one month to the next, and from one Sabbath to the next, all people will come to bow down to me—says Yahweh.
24 “Za su kuma fita su ga gawawwakin mutanen da suka yi mini tayarwa; tsutsotsin da suke cinsu ba za su taɓa mutuwa ba, balle wutar da take ƙona su ta mutu, za su kuma zama abin ƙyama ga dukan mutane.”
They will go out and see the dead bodies of the men who have rebelled against me, for the worms that eat them will not die, and the fire that consumes them will not be quenched; and it will be an abhorrence to all flesh.”

< Ishaya 66 >