< Ishaya 65 >

1 “Na bayyana kaina ga waɗanda ba su tambaye ni ba; ina samuwa ga waɗanda ba su neme ni ba. Ga al’ummar da ba tă kira bisa sunana ba, Na ce, ‘Ga ni, ga ni.’
[This is what Yahweh said]: “I was ready to reply [to my people], but no one requested me [to help them]. I was ready to help [even] those who did not call out to me. I continued to say, ‘I am here [to help you]!’
2 Dukan yini ina miƙa hannuwana ga mutane masu tayarwa, waɗanda suna tafiya a hanyoyin da ba su da kyau, suna bin tunaninsu,
[It is as though] I have continually held out my arms [to show that I am ready to help] my people who rebel [against me], and who [continually] do the evil things that they want to do.
3 mutanen da suna cin gaba da tsokanata a fuskata, suna miƙa hadayu a gonaki suna ƙone turare a bagadan tubali;
They boldly continue to do things that cause me to be angry: They offer sacrifices [to their idols] in their gardens, and they burn incense [to them] on [altars made of] bricks.
4 suna zama a kaburbura su kwana suna yin asirtattun ayyuka; suna cin naman aladu, tukwanensu kuma sun cika da nama marar tsabta;
They secretly remain awake at night in burial caves, [talking with the spirits of] ([dead people/their ancestors]). They eat the meat of pigs, and their pots are full of [other] meat that is [also] unacceptable to me.
5 suna cewa, ‘Ku tsaya a can; kada ku yi kusa da ni, gama na fi ku tsarki!’ Irin mutanen nan hayaƙi ne a hancina, wuta kuma da take cin gaba da ci dukan yini.
[Then] they say [to others], ‘Stay away from me; do not come near me, because I am very holy, [with the result that you should not touch me].’ People like that are [like] [MET] smoke in my nose [from] a fire that burns continually.
6 “Ga shi, yana nan a rubuce a gabana cewa ba zan ƙyale ba, zan yi cikakken ramuwa; zan yi ramuwa a cinyoyinsu
I have written [a record of all the evil things that they have done]. And I will not do nothing about all those things; I will certainly punish them
7 saboda zunubanku da kuma zunuban kakanninku,” in ji Ubangiji. “Gama sun ƙone turare a kan duwatsu suka kuma ƙazantar da ni a kan tuddai, zan yi musu awo in zuba a cinyoyinsu cikakken ramuwa saboda ayyukansu na dā.”
for the sins that they and their ancestors have committed. They have mocked/insulted me by burning incense [to their idols] on the hilltops. So I will punish them like they deserve for doing those things.”
8 Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kamar sa’ad da ruwan’ya’yan itace yana samuwa a cikin tarin’ya’yan inabi mutane kuma su ce, ‘Kada a lalace shi, har yanzu akwai abu mai kyau a ciki,’ haka nan zan yi a madadin bayina; ba zan hallaka su duka ba.
This is [also] what Yahweh said: “When there is a cluster of nice grapes on a vine, people do not throw them away, because they know that there is good juice in those grapes. Similarly, because there are some people [in Judah] who faithfully serve/worship me, I will not get rid of all of them.
9 Zan fitar da zuriyar Yaƙub, daga Yahuda kuma waɗanda za su mallaki duwatsuna; zaɓaɓɓun mutanena za su gāje su, a can kuma bayina za su zauna.
I will spare some of the descendants of Jacob who are living on the hills of Judah. I have chosen them, and they will possess that land; they will worship/serve me, and they will live there.
10 Sharon zai zama wurin kiwo don shanu, Kwarin Akor kuma wurin hutun garkuna, domin mutanena da suke nemana.
[Then all the land from the] Sharon [Plain near the Mediterranean Sea] and [as far east as] Achor Valley [near Jericho] will become pastureland where their cattle and sheep will rest.
11 “Amma game da ku waɗanda kuka yashe Ubangiji kuka manta da dutsena mai tsarki kuwa, ku da kuka shimfiɗa tebur don sa’a kuka kuma cika darunan ruwan inabin da aka dama don Ƙaddara,
But [it will be different] for you who have abandoned me, you who do not worship me on [Zion], my sacred hill, you who worship Gad and Meni, [the gods who you think will bring you] good luck and good fortune.
12 zan ƙaddara ku ga kaifin takobi, dukanku kuma za ku sunkuya wa mai yanka; gama na yi kira amma ba ku amsa ba, na yi magana amma ba ku saurara ba. Kuka aikata mugunta a gabana kuka kuma zaɓi abin da ba na jin daɗi.”
[It is I, not Meni, who will decide/say what will happen to you]; you will all [be slaughtered by] swords. [That will happen] because you did not answer when I called out to you. I spoke to you, but you did not pay attention. Instead, you did things that I said are evil; you chose to do things that do not please me.
13 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Bayin za su ci, amma ku za ku ji yunwa; bayina za su sha, amma ku za ku ji ƙishi; bayina za su yi farin ciki amma ku za ku sha kunya.
I, Yahweh the Lord, will give to those who worship and obey me things to eat and drink, and they will be happy; but [all] you evil people will be hungry and thirsty, and you will be [sad and] disgraced.
14 Bayina za su rera da farin cikin zukatansu, amma ku za ku yi kuka daga wahalar zuciya ku kuma yi kururuwa da karayar zuci.
Those who worship and obey me will sing joyfully, but you [evil people] will wail loudly because you will be suffering in your inner beings.
15 Za ku bar sunanku ga zaɓaɓɓuna yă zama abin la’antarwa; Ubangiji Mai Iko Duka zai kashe ku, amma ga bayina zai ba su wani suna.
Those whom I have chosen will use your names when they curse people; [I], Yahweh the Lord, will get rid of you. But I will give to those who worship and obey me a new name [that they will use when they bless people].
16 Duk wanda zai roƙi albarka a cikin ƙasar zai yi haka da gaskiyar Allah; wanda zai yi rantsuwa a cikin ƙasar zai rantse da gaskiyar Allah. Gama za a manta da wahalolin baya a kuma ɓoye su daga idanuna.
The people in this land have had many troubles, but I will cause those troubles to occur no more. Therefore those who ask me to bless them and those who solemnly promise to do something should never forget that I am God, who faithfully [do what I promise to do].”
17 “Ga shi, na halicci sabuwar sama da kuma sabuwar duniya. Abubuwa na dā za a manta da su, ba kuwa za a ƙara tuna da su ba.
“Note this: [Some day] I will create a new heaven and a new earth. [They will be very wonderful, with the result that] you will no longer think about all [the troubles] you had previously.
18 Amma ku yi murna ku kuma yi farin ciki har abada a abin da na halitta, gama zan halicci Urushalima ta zama abin murna mutanenta kuwa abin farin ciki.
Be glad and always rejoice because of what I will do: Jerusalem will be a place where [people] rejoice; the people who live there will always be happy.
19 Zan yi farin ciki a kan Urushalima in kuma yi murna saboda mutanena; a can ba za a ƙara jin karar makoki da na kuka ba.
I will rejoice about Jerusalem, and I will be delighted with my people. [People] will no longer weep or cry because of being distressed.
20 “A cikinta ba za a ƙara jin jariri ya rayu na’yan kwanaki kawai ba, ko kuwa wani tsohon da bai cika kwanakinsa ba; duk wanda ya mutu yana da shekaru ɗari za a ce ya mutu a kurciya ne kawai; duk wanda bai kai ɗari ba za a ɗauka la’antacce ne.
No child will die when it is still an infant; all people will live until they are very old. [People will consider that] anyone who is 100 years old is still young; [they will consider that] anyone who dies who is younger than that has been cursed.
21 Za su gina gidaje su kuma zauna a cikinsu; za su yi shuki a gonakin inabi su kuma ci’ya’yansu.
My people will build houses and [then] live in them. They will plant vineyards and then eat grapes from those vineyards.
22 Ba za su ƙara gina gidaje waɗansu kuma su zauna a cikinsu ba, ko su yi shuki waɗansu kuma su ci ba. Gama kamar yadda kwanakin itace suke, haka kwanakin mutanena za su kasance; zaɓaɓɓuna za su daɗe suna jin daɗin ayyukan hannuwansu.
As for the houses that they build, no one will [take those houses away from them and] live in them. No one will take a vineyard away from its owner. My chosen people will live a long time, like trees do, and they will enjoy what they have accomplished— [the houses that they have built and the crops that they have planted].
23 Ba za su yi wahala a banza ba ko su haifi’ya’yan da aka ƙaddara da rashin sa’a; gama za su zama mutanen da Ubangiji ya yi wa albarka, su da zuriyarsu tare da su.
They will not work hard in vain, and their children will not die from some (calamity/terrible thing happening to them). I will [certainly] bless their children and their grandchildren.
24 Kafin su yi kira zan amsa; yayinda suke cikin magana zan ji.
Before they call to me [to help them], I will answer; I will answer their prayers while they are still praying [for me to do something for them].
25 Kyarketai da’yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci buɗu kamar yadda shanu suke yi, amma ƙura ce za tă zama abincin maciji. Ba za su ƙara cuci ko su yi ɓarna a kan dukan dutsena mai tsarki ba,” in ji Ubangiji.
No one will be harmed or injured anywhere on [Zion], my sacred hill: Wolves and lambs will eat grass together [peacefully]; lions will eat hay like oxen do, [and they will not attack people]. Snakes will [not hurt anyone; they will lie on the ground and] eat [only] dirt. [That is surely what it will be like because I], Yahweh, have said it.”

< Ishaya 65 >