< Ishaya 27 >

1 A wannan rana, Ubangiji zai yi hukunci da takobi, takobinsa mai tsanani, mai ƙarfi da kuma mai muguwar ɓarna, zai hukunta dodon ruwa macijin nan da ya kanannaɗe, dodon ruwa macijin nan mai murɗewa; zai kashe dodon nan na teku.
En ce jour-là l'Eternel punira de sa dure et grande et forte épée, le Léviathan, le serpent traversant; le Léviathan, dis-je serpent tortu, et il tuera la baleine qui [est] dans la mer.
2 A wannan rana, “Ku rera game da gonar inabi mai ba da’ya’ya ku ce
En ce jour-là chantez, vous entre-répondant l'un à l'autre, touchant la vigne [fertile] en vin rouge.
3 Ni, Ubangiji na lura da ita; na yi ta yin mata banruwa. Na yi tsaronta dare da rana don kada wani yă yi mata ɓarna.
C'est moi l'Eternel qui la garde, je l'arroserai de moment en moment, je la garderai nuit et jour, afin que personne ne lui fasse du mal.
4 Ban yi fushi ba. Da a ce ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne suke kalubalanta na mana! Zan fita in yi yaƙi da su; da na sa musu wuta duka.
Il n'y a point de fureur en moi; qui m'opposera des ronces et des épines pour les combattre? je marcherai sur elles, je les brûlerai toutes ensemble.
5 Ko kuma bari su zo wurina don mafaka; bari su yi sulhu da ni, I, bari su yi sulhu da ni.”
Ou forcerait-il ma force? Qu'il fasse la paix avec moi, qu'il fasse la paix avec moi.
6 A kwanaki masu zuwa Yaƙub zai yi saiwa, Isra’ila zai yi toho ya kuma yi fure ya cika dukan duniya da’ya’ya.
Il fera ci-après que Jacob prendra racine; Israël boutonnera, et s'épanouira; et ils rempliront de fruit le dessus de la terre habitable.
7 Ubangiji ya buge shi kamar yadda ya bugi waɗanda suka buge shi? An kashe shi kamar yadda aka kashe waɗanda suka kashe shi?
L'aurait-il frappé de la même plaie dont il frappe celui qui l'a frappé? et aurait-il été tué comme ont été tués ceux qu'il a tués?
8 Ta wurin yaƙi da zaman bauta ka hukunta shi, da tsananin tsawa kuma ka kore shi, kamar a ranar da iskar gabas ta hura.
Tu plaideras avec elle modérément, quand tu la renverras; [même quand] il ferait retentir son vent rude, au jour du vent d'Orient.
9 A ta haka fa, za a yi kafarar laifin Yaƙub, wannan kuma zai zama cikakken amfanin kau da zunubinsa. Sa’ad da ya niƙa duwatsun bagade suka zama kamar allin da aka farfashe kucu-kucu, har ba sauran ginshiƙan Ashera ko bagadan ƙona turare da za a bari a tsaye.
C'est pourquoi l'expiation de l'iniquité de Jacob sera faite par ce moyen, et ceci en sera le fruit entier, que son péché sera ôté; quand il aura mis toutes les pierres de l'autel comme des pierres de plâtre menuisées, et lorsque les bocages, et les tabernacles ne seront plus debout.
10 Birni mai katanga ya zama kufai, yasasshen mazauni, an yashe shi kamar hamada; a can’yan maruƙa suke kiwo, a can suke kwance; sun kakkaɓe rassanta ƙaf.
Car la ville munie sera désolée, le logement agréable sera abandonné et délaissé comme un désert, le veau y paîtra, il y gîtera, et il broutera les branches qui y seront.
11 Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
Quand son branchage sera sec il sera brisé, et les femmes y venant en allumeront du feu; car ce n'est pas un peuple intelligent, c'est pourquoi celui qui l'a fait n'aura point pitié de lui, et celui qui l'a formé ne lui fera point de grâce.
12 A wannan rana Ubangiji zai tankaɗe daga Yuferites mai gudu zuwa Rafin Masar, ku kuma, ya Isra’ilawa, za a tattara ku ɗaya-ɗaya.
Il arrivera donc en ce jour-là, que l'Eternel secouera depuis le cours du fleuve, jusqu'au torrent d'Egypte; mais vous serez glanés un à un, ô enfants d'Israël.
13 Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
Et il arrivera en ce jour-là, qu'on sonnera du grand cor, et ceux qui s'étaient perdus au pays d'Assyrie, et ceux qui avaient été chassés au pays d'Egypte, reviendront, et se prosterneront devant l'Eternel, en la sainte montagne, à Jérusalem.

< Ishaya 27 >