< Ishaya 21 >

1 Abin da Allah ya faɗa game da Hamada da take kusa da Teku. Kamar guguwa mai share cikin ƙasar kudu, mai hari ya zo daga hamada, daga ƙasar mai banrazana.
The oracle of the wilderness of the sea. As whirlwinds in the Negev sweep through, it comes from the wilderness, from an awesome land.
2 An nuna mini mugun wahayi, mai bashewa ya bashe, mai washewa ya washe. Elam, ki yi yaƙi! Mediya, ki yi kwanto! Zan kawo ƙarshen dukan nishe-nishen da ta jawo.
A grievous vision is declared to me. The treacherous man deals treacherously, and the destroyer destroys. Go up, Elam; attack. I have stopped all of Media's sighing.
3 Game da wannan jikina yana ciwo, zafi ya kama ni, kamar na mace mai naƙuda; na razana game da abin da na ji, na yi mamakin abin da na gani.
Therefore my thighs are filled with anguish. Pains have taken hold on me, like the pains of a woman in labor. I am in so much pain that I can't hear. I so am dismayed that I can't see.
4 Gabana tana ta fāɗuwa, tsoro ya sa ina rawan jiki; hasken da nake marmari ya zo da razana gare ni.
My heart flutters. Horror has frightened me. The twilight that I desired has been turned into trembling for me.
5 Sun shirya teburori, sun shimfiɗa dardumai, sun ci, sun sha! Tashi, ku hafsoshi, sa mai a garkuwoyi!
They prepare the table. They set the watch. They eat. They drink. Rise up, you princes, oil the shield.
6 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Tafi, ka sa mai tsaro ka kuma sa ya ba da rahoton abin da ya gani.
For the LORD said to me, "Go, set a watchman. Let him declare what he sees.
7 Sa’ad da ya ga kekunan yaƙi tare da ƙungiyoyin dawakai, mahaya a kan jakuna, ko mahaya a kan raƙuma, to, fa ya zauna a faɗake, ya kintsa sosai.”
When he sees chariots, horsemen in pairs, riders on donkeys, riders on camels, let him listen diligently, very diligently."
8 Mai tsaron kuma ya yi ihu, “Kowace rana, ranka yă daɗe, nakan tsaya a hasumiyar tsaro; kowane dare nakan tsaya a wurin aikina.
Then the lookout shouted: "Lord, I stand continually on the watchtower in the daytime, and every night I stay at my post.
9 Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’”
Look, here comes a troop of men, horsemen in pairs." He answered, "Fallen, fallen is Babylon; and all the engraved images of her gods are broken to the ground.
10 Ya mutanena, an ragargaje ku a masussuka, na faɗa muku abin da na ji daga Ubangiji Maɗaukaki, daga Allah na Isra’ila.
You are my threshing, and the grain of my floor." That which I have heard from the LORD of hosts, the God of Israel, I have declared to you.
11 Abin da Allah ya faɗa game da Duma, Wani ya kira ni daga Seyir, “Mai tsaro, me ya rage a daren? Mai tsaro, me ya rage a daren?”
The burden of Dumah. One calls to me out of Seir, "Watchman, what of the night? Watchman, what of the night?"
12 Mai tsaro ya amsa, “Safiya ta gabato, haka kuma dare. In za ka yi tambaya, to, yi tambaya; sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”
The watchman said, "The morning comes, and also the night. If you will inquire, inquire. Come back again."
13 Abin da Allah ya faɗa game da Arabiya. Ku ayarin Dedanawa, ku da kuka sauka a jejin Arabiya,
The burden on Arabia. In the forest in Arabia you will lodge, you caravans of Dedanites.
14 ku kawo ruwa don ƙishirwa; ku da kuke zama a Tema, ku kawo abinci don masu gudun hijira.
They brought water to him who was thirsty. The inhabitants of the land of Tema met the fugitives with their bread.
15 Sun gudu daga takobi, daga takobin da aka janye, daga bakan da aka tanƙware da kuma daga zafin yaƙi.
For they fled away from the swords, from the drawn sword, from the bent bow, and from the heat of battle.
16 Ga abin da mai girma ya ce mini, “Cikin shekara ɗaya, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, dukan sojojin Kedar za su zo ga ƙarshe.
For the LORD said to me, "Within a year, as a worker bound by contract would count it, the glory of Kedar will fail,
17 Waɗanda suka yi rai na maharba, jarumawan Kedar, za su zama kaɗan.” Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa.
and the residue of the number of the archers, the warriors of the people of Kedar, will be few; for the LORD, the God of Israel, has spoken it."

< Ishaya 21 >