< Ishaya 1 >

1 Wahayi game da Yahuda da Urushalima wanda Ishaya ɗan Amoz ya gani a zamanin da Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, suka yi mulkin Yahuda.
رویای اشعیا ابن آموص که آن را درباره یهودا و اورشلیم، در روزهای عزیا و یوتام و آحاز و حزقیا پادشاهان یهودا دید.۱
2 Ku kasa kunne, ya sammai! Ki saurara, ya duniya! Gama Ubangiji ya yi magana, “Na yi renon’ya’ya, na kuma raya su, amma sun tayar mini.
‌ای آسمان بشنو و‌ای زمین گوش بگیر زیراخداوند سخن می‌گوید. پسران پروردم وبرافراشتم اما ایشان بر من عصیان ورزیدند.۲
3 Saniya ta san maigidanta, jaki ya san wurin sa wa dabbobi abinci maigidansa, amma Isra’ila ba su sani, mutanena ba su gane ba.”
گاومالک خویش را و الاغ آخور صاحب خود رامی شناسد، اما اسرائیل نمی شناسند و قوم من فهم ندارند.۳
4 Kash, ya ke al’umma mai zunubi, mutane cike da laifi, tarin masu aikata mugunta,’ya’yan da aka miƙa wa lalaci! Sun yashe Ubangiji; sun rena Mai Tsarkin nan na Isra’ila suka juya masa baya.
وای بر امت خطاکار و قومی که زیربار گناه می‌باشند و بر ذریت شریران و پسران مفسد. خداوند را ترک کردند و قدوس اسرائیل رااهانت نمودند و بسوی عقب منحرف شدند.۴
5 Me ya sa za a ƙara yin muku dūka? Me ya sa kuka nace ga yin tayarwa? An yi wa dukan kanku rauni, zuciyarku duk tana ciwo.
چرا دیگر ضرب یابید و زیاده فتنه نمایید؟ تمامی سر بیمار است و تمامی دل مریض.۵
6 Daga tafin ƙafarku zuwa saman kanku ba lafiya, sai miyaku da ƙujewa da manyan gyambuna, ba a tsabtacce su ba ko a daure ko shafa musu magani.
ازکف پا تا به‌سر در آن تندرستی نیست بلکه جراحت و کوفتگی و زخم متعفن، که نه بخیه شده و نه بسته گشته و نه با روغن التیام شده است.۶
7 Ƙasarku ta zama kufai, an ƙone biranenku da wuta; baƙi suna ƙwace gonakinku a idanunku, ta zama kango kamar sa’ad da baƙi suka rushe ta.
ولایت شما ویران و شهرهای شما به آتش سوخته شده است. غریبان، زمین شما را در نظرشما می‌خورند و آن مثل واژگونی بیگانگان خراب گردیده است.۷
8 An bar diyar Sihiyona kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, kamar bukka a gonar kabewa, kamar birnin da aka kewaye da yaƙi.
و دختر صهیون مثل سایه بان در تاکستان و مانند کپر در بوستان خیار ومثل شهر محاصره شده، متروک است.۸
9 Da ba a ce Ubangiji Maɗaukaki ya bar mana raguwar masu rai ba, da mun zama kamar Sodom, da mun zama kamar Gomorra.
اگر یهوه صبایوت بقیه اندکی برای ما وا نمی گذاشت، مثل سدوم می‌شدیم و مانند عموره می‌گشتیم.۹
10 Ku saurari maganar Ubangiji, ku masu mulkin Sodom; ku kasa kunne ga dokar Allahnmu, ku mutanen Gomorra!
‌ای حاکمان سدوم کلام خداوند را بشنویدو‌ای قوم عموره شریعت خدای ما را گوش بگیرید.۱۰
11 Ubangiji ya ce, “Yawan hadayunku, mene ne suke a gare ni?” Ina da isashen hadayun ƙonawa, na raguna da na kitsen dabbobi masu ƙiba; ba na jin daɗin jinin bijimai da na tumaki da kuma na awaki.
خداوند می‌گوید از کثرت قربانی های شما مرا چه فایده است؟ از قربانی های سوختنی قوچها و پیه پرواریها سیر شده‌ام و به خون گاوان و بره‌ها و بزها رغبت ندارم.۱۱
12 Sa’ad da kuka zo don ku bayyana a gabana, wa ya nemi wannan daga gare ku, da kuke kai da kawowa a filayen gidana?
وقتی که می‌آیید تابه حضور من حاضر شوید، کیست که این را ازدست شما طلبیده است که دربار مرا پایمال کنید؟۱۲
13 Ku daina kawo hadayu marasa amfani! Turarenku abin ƙyama ne gare ni. Ina ƙin bukukkuwanku na Sabon Wata, da na ranakun Asabbaci, da taronku na addini, ba zan iya jure wa mugun taronku ba.
هدایای باطل دیگر میاورید. بخور نزدمن مکروه است و غره ماه و سبت و دعوت جماعت نیز. گناه را با محفل مقدس نمی توانم تحمل نمایم.۱۳
14 Bukukkuwanku na Sabon Wata da na tsarkakan ranaku na ƙi su. Sun zama mini kaya; na gaji da ɗaukansu.
غره‌ها و عیدهای شما را جان من نفرت دارد؛ آنها برای من بار سنگین است که ازتحمل نمودنش خسته شده‌ام.۱۴
15 Sa’ad da kuka ɗaga hannuwanku wajen yin addu’a, zan ɓoye fuskata daga gare ku; ko da kun miƙa addu’o’i masu yawa, ba zan kasa kunne ba. Hannuwanku sun cika da jini!
هنگامی که دستهای خود را دراز می‌کنید، چشمان خود را ازشما خواهم پوشانید و چون دعای بسیارمی کنید، اجابت نخواهم نمود زیرا که دستهای شما پر از خون است.۱۵
16 Ku yi wanka ku kuma tsabtacce kanku. Ku kawar da mugayen ayyukanku daga gabana; Ku daina aikata mugunta.
خویشتن را شسته، طاهرنمایید و بدی اعمال خویش را از نظر من دورکرده، از شرارت دست بردارید.۱۶
17 Ku koyi yin nagarta; ku nemi adalci. Ku ƙarfafa waɗanda aka zalunta. Ku ba wa marayu hakkinsu, ku taimaki gwauruwa.
نیکوکاری رابیاموزید و انصاف را بطلبید. مظلومان را رهایی دهید. یتیمان را دادرسی کنید و بیوه‌زنان راحمایت نمایید.۱۷
18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa ku zo, bari mu dubi batun nan tare, Ko da zunubanku sun yi ja kamar garura, za su zama fari kamar ƙanƙara; ko da sun yi ja kamar mulufi, za su zama kamar ulu.
خداوند می‌گوید بیایید تا با همدیگر محاجه نماییم. اگر گناهان شما مثل ارغوان باشد مانند برف سفید خواهد شد و اگرمثل قرمز سرخ باشد، مانند پشم خواهد شد.۱۸
19 In kuna da niyya kuna kuma yi mini biyayya, za ku ci abubuwa masu kyau daga ƙasar;
اگر خواهش داشته، اطاعت نمایید، نیکویی زمین را خواهید خورد.۱۹
20 amma in kuka yi tsayayya kuka kuma yi tayarwa, za a kashe ku da takobi.” Ni Ubangiji na faɗa.
اما اگر ابا نموده، تمردکنید شمشیر شما را خواهد خورد زیرا که دهان خداوند چنین می‌گوید.۲۰
21 Dubi yadda amintacciyar birni ta zama karuwa! Dā ta cika da yin gaskiya; dā masu adalci a can suke zama, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai!
شهر امین چگونه زانیه شده است. آنکه ازانصاف مملو می‌بود و عدالت در وی سکونت می‌داشت، اما حال قاتلان.۲۱
22 Azurfarki ta zama jebu, an gauraye ruwan inabinki mafi kyau da ruwa.
نقره تو به درد مبدل شده، و شراب تو از آب ممزوج گشته است.۲۲
23 Masu mulkinki’yan tawaye ne, abokan ɓarayi; dukansu suna ƙaunar cin hanci suna bin kyautai. Ba sa taɓa tsare marayu a ɗakin shari’a; ba sa taimakon gwauruwa.
سروران تو متمرد شده و رفیق دزدان گردیده، هریک از ایشان رشوه را دوست می‌دارند و در‌پی هدایا می‌روند. یتیمان را دادرسی نمی نمایند ودعوی بیوه‌زنان نزد ایشان نمی رسد.۲۳
24 Saboda haka Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, Mai Iko nan na Isra’ila, ya furta, “Kai, zan sami hutu daga maƙiyana in kuma yi ramuwa a kan abokan gābana.
بنابراین، خداوند یهوه صبایوت، قدیر اسرائیل می‌گویدهان من از خصمان خود استراحت خواهم یافت واز دشمنان خویش انتقام خواهم کشید.۲۴
25 Zan juye hannuna a kanki; zan wanke ke sarai in fitar da dukan ƙazantarki.
ودست خود را بر تو برگردانیده، درد تو را بالکل پاک خواهم کرد، و تمامی ریمت را دور خواهم ساخت.۲۵
26 Zan maido da alƙalanki kamar yadda suke a dā can, mashawartanki kamar yadda suke da fari. Bayan haka za a ce da ke Birnin Masu Adalci, Amintacciyar Birni.”
و داوران تو را مثل اول و مشیران تو رامثل ابتدا خواهم برگردانید و بعد از آن، به شهرعدالت و قریه امین مسمی خواهی شد.۲۶
27 Za a fanshi Sihiyona da adalci, masu tubanta kuma da aikin gaskiya.
صهیون به انصاف فدیه داده خواهد شد وانابت کنندگانش به عدالت.۲۷
28 Amma za a karye’yan tawaye da masu zunubi, waɗanda suka rabu da Ubangiji kuma za su hallaka.
و هلاکت عاصیان و گناهکاران با هم خواهد شد و آنانی که خداوندرا ترک نمایند، نابود خواهند گردید.۲۸
29 “Za ku ji kunya saboda masujadan ƙarƙashin itatuwan oak da kuka yi farin ciki; za a kunyata ku saboda lambun da kuka zaɓa.
زیراایشان از درختان بلوطی که شما خواسته بودیدخجل خواهند شد و از باغاتی که شما برگزیده بودید رسوا خواهند گردید.۲۹
30 Za ku zama kamar itacen oak mai busasshen ganyaye, kamar lambu marar ruwa.
زیرا شما مثل بلوطی که برگش پژمرده و مانند باغی که آب نداشته باشد خواهید شد.۳۰
31 Mutum mai ƙarfi zai zama kamar rama, aikinsa kuma kamar tartsatsin wuta; duka za su ƙone tare, ba kuwa wanda zai kashe wutar.”
و مرد زورآور پرزه کتان و عملش شعله خواهد شد و هردوی آنها باهم سوخته خواهند گردید و خاموش کننده‌ای نخواهد بود.۳۱

< Ishaya 1 >