< Hosiya 7 >

1 a duka sa’ad da zan warkar da Isra’ila, zunuban Efraim za su tonu za a kuma bayyana laifofin Samariya. Suna ruɗu, ɓarayi sukan fasa su shiga gidaje,’yan fashi sukan yi fashi a tituna;
when I would heal Israel, then Ephrain’s guilt is revealed, and Samaria’s crimes are seen, how they practise fraud and the thief enters in, while outside bandits plunder.
2 amma ba su gane cewa na tuna da dukan ayyukan muguntarsu ba. Zunubansu sun kewaye su; kullum suna a gabana.
But it never crosses their minds that I remember their wickedness. Now their misdeeds surround them, they are always before my face.
3 “Suna faranta wa sarki zuciya da muguntarsu, shugabanni kuma da ƙarairayinsu.
Their wickedness amuses the king, and their lying gladdens the princes,
4 Dukansu mazinata ne suna ƙuna kamar matoya wadda mai gashin burodi ba ya bukata yă tura mata wuta daga cuɗe kullu har kumburinsa.
since they are all of them adulterers. Their desire to do evil burns like an oven heated by the baker, so hot that he need not stir the fire, from the kneading of the dough, until it rises.
5 A ranar bikin sarkinmu shugabanni sukan bugu da ruwan inabi, yă yi cuɗanya da masu ba’a.
On our king’s festival day, the princes are flushed with fever from wine. He stretched forth his hand with the contemptuous,
6 Zukatansu suna kamar matoya; sukan kusace shi da wayo. Muguwar aniyarsu takan yi ta ci dukan dare; da safe sai ta ƙuna kamar harshen wuta.
for like an oven their heart burns with treachery, all night their anger smoulders, in the morning it blazes into a flame of fire.
7 Dukansu suna da zafi kamar matoya; suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sukan fāɗi, kuma babu waninsu da yake kira gare ni.
All of them glow like an oven, they devour their rulers. All their kings have fallen. There is none among them who calls to me.
8 “Efraim yana cuɗanya da al’ummai; Efraim waina ne mai fāɗi da ba a juye ba.
Ephraim – he lets himself be mixed among the peoples, Ephraim – he has become a cake unturned.
9 Baƙi sun tsotse ƙarfinsa, amma bai gane ba. Gashi kansa ya cika da furfura, amma bai lura ba.
Strangers have devoured his strength, but he does not know it. His hair is sprinkled with grey, but he does not notice.
10 Girmankan Isra’ila ya ba da shaida a kansa, amma duk da haka bai dawo ga Ubangiji Allahnsa ko yă neme shi ba.
Israel’s arrogance testifies against them yet they do not return to the Lord their God, and in all this they do not seek him.
11 “Efraim yana kama da kurciya, marar wayo, marar hankali, yanzu yana kira ga Masar, yanzu yana juyewa ga Assuriya.
Ephraim is like a simple, silly dove: to Egypt they call, after Assyria they go,
12 Sa’ad da suka tafi, zan jefa ragata a kansu; zai janye su ƙasa kamar tsuntsayen sararin sama. Sa’ad da na ji suna tafiya tare, zan kama su.
wherever they turn I will spread my net over them, like birds of the sky I will bring them down, I will catch them when I hear them gathering.
13 Kaitonsu, domin sun kauce daga gare ni! Hallaka za tă aukar musu, domin sun tayar mini! Na ƙudura in cece su amma suna faɗar ƙarya a kaina.
Woe to them, for they have strayed from me! Destruction to them, for they have been untrue to me. Although it was I who redeemed them, they speak lies about me.
14 Ba sa yin mini kuka da zuciyarsu amma suna ihu a kan gadajensu. Sukan taru wurin ɗaya don hatsi da ruwan inabi amma su juya mini baya.
They have never cried to me with their hearts, but they are always wailing on their beds. They gather to beg for corn and new wine, but they turn away from me.
15 Na horar da su na kuma ƙarfafa su, amma sun ƙulla mini maƙarƙashiya.
Although it was I who trained and strengthened their arms, concerning me they plan only evil.
16 Ba sa juya ga Mafi Ɗaukaka; suna kama da tanƙwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi saboda banzan maganganunsu. Saboda wannan za a wulaƙanta su a ƙasar Masar.
They turn away from the Most High. They have become like a bow that swerves. Their princes will fall by the sword, because of the insolence of their tongues. The land of Egypt will mock them.

< Hosiya 7 >