< Farawa 50 >

1 Yusuf kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya kuma sumbace shi.
И припад Иосиф на лице отца своего, плакася (горько) о нем и облобыза его:
2 Sa’an nan Yusuf ya umarci masu maganin da suke yin masa hidima, su shafe mahaifinsa Isra’ila da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe shi da maganin hana ruɓa.
и повеле Иосиф рабом своим погребателем погребсти отца своего. И погребоша погребателие Израиля.
3 Suka ɗauki kwana arba’in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi makoki dominsa kwana saba’in.
И исполнишася ему четыредесять дний: тако бо исчисляются дние погребения: и плакася его Египет седмьдесят дний.
4 Sa’ad da kwanakin makoki suka wuce, sai Yusuf ya ce wa iyalin gidan Fir’auna, “In na sami tagomashi a idanunku, ku yi magana da Fir’auna domina. Ku faɗa masa,
Егда же преидоша дние плача, глагола Иосиф ко вельможам фараоновым, глаголя: аще обретох благодать пред вами, рцыте о мне во ушы фараону, глаголюще:
5 ‘Mahaifina ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, “Ina gab da mutuwa, ka binne ni a kabarin da na haƙa wa kaina a ƙasar Kan’ana.” Yanzu fa bari in haura in binne mahaifina, sa’an nan in dawo.’”
отец мой закля мя прежде скончания (своего), глаголя: во гробе, егоже ископах себе в земли Ханаани, тамо мя погреби: ныне убо возшед погребу отца моего и возвращуся. И рекоша фараону по словеси Иосифову.
6 Fir’auna ya ce, “Haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya sa ka rantse za ka yi.”
И рече фараон ко Иосифу: взыди, погреби отца твоего, якоже закля тя.
7 Saboda haka Yusuf ya haura don yă binne mahaifinsa. Dukan hafsoshin Fir’auna suka yi masa rakiya tare da manyan mutanen gidan Fir’auna, da kuma dukan manyan mutanen Masar
И взыде Иосиф погребсти отца своего. И совзыдоша с ним вси раби фараони и старейшины дому его, и вси старейшины земли Египетския,
8 da kuma dukan membobin gidan Yusuf, da’yan’uwansa da kuma waɗanda suke na gidan mahaifinsa. Yara kaɗai da garkunansu da kuma shanunsu ne aka bari a Goshen.
и весь дом Иосифов и братия его, и весь дом отца его и сродницы его: овцы же и волы оставиша в земли Гесем.
9 Kekunan yaƙi da mahayan dawakai su ma suka haura tare da shi. Babbar ƙungiya jama’a ce ƙwarai.
И совзыдоша с ним и колесницы и конницы, и бысть полк велик зело.
10 Sa’ad da suka kai masussukar Atad, kusa da Urdun, sai suka yi kuka da ƙarfi da kuma mai zafi, a can Yusuf ya yi makoki kwana bakwai saboda mahaifinsa.
И приидоша на Гумно Атадово, еже есть об он пол Иордана, и рыдаша его рыданием велиим и крепким зело: и сотвори плачь отцу своему седмь дний.
11 Sa’ad da Kan’aniyawa waɗanda suke zama a can suka ga makokin a masussukan Atad, sai suka ce, “Masarawa suna bikin makoki na musamman.” Shi ya sa ake kira wannan wurin da yake kusa da Urdun, Abel-Mizrayim.
И видеша жителие земли Ханаанския плачь на Гумне Атадове и реша: плачь велик сей есть Египтяном. Сего ради наречеся имя месту тому плачь Египетск, еже есть об он пол Иордана.
12 Haka fa’ya’yan Yaƙub maza suka yi yadda ya umarce su.
И сотвориша ему тако сынове его, якоже заповеда им.
13 Suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan’ana suka kuma binne shi a kogon da yake cikin filin Makfela, kusa da Mamre, wanda Ibrahim ya saya tare da filin, ya zama makabarta daga Efron mutumin Hitti.
И взяша его сынове его в землю Ханааню и погребоша его в пещере Сугубей, юже стяжа Авраам пещеру в стяжание гроба от Ефрона Хеттеанина, прямо Мамврии.
14 Bayan ya binne mahaifinsa, sai Yusuf ya koma Masar, tare da’yan’uwansa da kuma dukan waɗanda suka tafi tare da shi don binne mahaifinsa.
И возвратися Иосиф во Египет, сам и братия его и вси совозшедшии погребсти отца его.
15 Sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka ga cewa mahaifinsu ya mutu, sai suka ce, “Mai yiwuwa Yusuf yana riƙe da mu a zuciya, wataƙila zai rama dukan abubuwa marasa kyau da muka yi masa?”
Видевше же братия Иосифовы, яко умре отец их, реша: да не когда воспомянет злобу нашу Иосиф и воздаянием воздаст нам за вся злая, яже показахом ему.
16 Saboda haka suka aika wa Yusuf suna cewa, “Mahaifinka ya bar waɗannan umarnai kafin yă rasu.
И пришедше ко Иосифу рекоша: отец твой закля прежде кончины своея, глаголя:
17 Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
тако рцыте Иосифу: остави им неправду и грех их, яко лукавая тебе показаша: и ныне приими неправду рабов Бога отца твоего. И плакася Иосиф, глаголющим им к нему.
18 ’Yan’uwansa kuwa suka zo suka fāɗi a gabansa suka ce, “Mu bayinka ne.”
И пришедше к нему рекоша: се, мы тебе раби.
19 Amma Yusuf ya ce musu, “Kada ku ji tsoro. Ni Allah ne?
И рече к ним Иосиф: не бойтеся, Божий бо есмь аз:
20 Kun yi niyya ku yi mini lahani, amma Allah ya nufe wannan ya zama alheri don yă cika abin da yanzu yake faruwa, ceton rayuka masu yawa.
вы совещасте на мя злая, Бог же совеща о мне благая, дабы было якоже днесь, и препиталися бы людие мнози.
21 Saboda haka, kada ku ji tsoro. Zan tanada muku da kuma’ya’yanku.” Ya sāke tabbatar musu, ya kuma yi musu magana ta alheri.
И рече им: не бойтеся, аз препитаю вас и домы вашя. И утеши их, и глагола им по сердцу их.
22 Yusuf ya zauna a Masar tare da dukan iyalin mahaifinsa. Ya rayu shekara ɗari da goma.
И вселися Иосиф во Египте сам и братия его и весь дом отца его: и поживе Иосиф лет сто десять.
23 Ya kuma ga tsara ta uku ta’ya’yan Efraim. Haka ma’ya’yan Makir ɗan Manasse, an haife su aka sa a gwiwoyin Yusuf.
И виде Иосиф Ефремли дети до третияго рода: и сынове Махира сына Манассиина родишася при бедрех Иосифовых.
24 Sai Yusuf ya ce wa’yan’uwansa, “Ina gab da mutuwa. Amma tabbatacce Allah zai taimake ku, yă fid da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub.”
И рече Иосиф братии своей, глаголя: аз умираю, посещением же посетит вас Бог и изведет вас от земли сея в землю, о нейже клятся Бог отцем нашым Аврааму, Исааку и Иакову.
25 Yusuf kuwa ya sa’ya’yan Isra’ila maza suka yi rantsuwa, ya kuma ce, “Tabbatacce Allah zai taimake ku, ku kuma dole ku ɗauki ƙasusuwana, ku haura da su daga wannan wuri.”
И закля Иосиф сыны Израилевы, глаголя: в посещении, имже посетит вас Бог, совознесите и кости моя отсюду с вами.
26 Yusuf kuwa ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Bayan an shafe shi da maganin hana ruɓa, sai aka sa shi a akwatin gawa a Masar.
И скончася Иосиф сый лет ста десяти: и погребоша его, и положиша в раце во Египте.

< Farawa 50 >