< Farawa 5 >

1 Wannan shi ne rubutaccen tarihin zuriyar Adamu. Sa’ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin kamannin Allah.
Hic est liber generationis Adam. In die, qua creavit Deus hominem, ad similitudinem Dei fecit illum.
2 Ya halicce su namiji da ta mace, ya kuma albarkace su. Sa’ad da kuma aka halicce su, ya kira su “Mutum.”
Masculum et feminam creavit eos, et benedixit illis: et vocavit nomen eorum Adam, in die quo creati sunt.
3 Sa’ad da Adamu ya yi shekaru 130, sai ya haifi ɗa wanda ya yi kama da shi, ya kuma kira shi Set.
Vixit autem Adam centum triginta annis: et genuit ad imaginem et similitudinem suam, vocavitque nomen eius Seth.
4 Bayan an haifi Set, Adamu ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et facti sunt dies Adam, postquam genuit Seth, octingenti anni: genuitque filios et filias.
5 Gaba ɗaya dai, Adamu ya yi shekaru 930, sa’an nan ya mutu.
Et factum est omne tempus quod vixit Adam, anni nongenti triginta, et mortuus est.
6 Sa’ad da Set ya yi shekara 105, sai ya haifi Enosh.
Vixit quoque Seth centum quinque annis, et genuit Enos.
7 Bayan ya haifi Enosh, Set ya yi shekara 807, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Vixitque Seth postquam genuit Enos, octingentis septem annis, genuitque filios et filias.
8 Gaba ɗaya dai, Set ya yi shekaru 912, sa’an nan ya mutu.
Et facti sunt omnes dies Seth nongentorum duodecim annorum, et mortuus est.
9 Sa’ad da Enosh ya yi shekara 90, sai ya haifi Kenan.
Vixit vero Enos nonaginta annis, et genuit Cainan.
10 Bayan ya haifi Kenan, Enosh ya yi shekara 815, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Post cuius ortum vixit octingentis quindecim annis, et genuit filios, et filias.
11 Gaba ɗaya dai, Enosh ya yi shekaru 905, sa’an nan ya mutu.
Factique sunt omnes dies Enos nongenti quinque anni, et mortuus est.
12 Sa’ad da Kenan ya yi shekara 70, sai ya haifi Mahalalel.
Vixit quoque Cainan septuaginta annis, et genuit Malaleel.
13 Bayan ya haifi Mahalalel, Kenan ya yi shekara 840, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
Et vixit Cainan, postquam genuit Malaleel, octingentis quadraginta annis, genuitque filios et filias.
14 Gaba ɗaya dai, Kenan ya yi shekara 910, sa’an nan ya mutu.
Et facti sunt omnes dies Cainan nongenti decem anni, et mortuus est.
15 Sa’ad da Mahalalel ya yi shekara 65, sai ya haifi Yared.
Vixit autem Malaleel sexaginta quinque annis, et genuit Iared.
16 Bayan ya haifi Yared, Mahalalel ya yi shekara 830, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata
Et vixit Malaleel postquam genuit Iared, octingentis triginta annis: et genuit filios et filias.
17 Gaba ɗaya dai, Mahalalel ya yi shekara 895, sa’an nan ya mutu.
Et facti sunt omnes dies Malaleel octingenti nonaginta quinque anni, et mortuus est.
18 Sa’ad da Yared ya yi shekara 162, sai ya haifi Enok.
Vixitque Iared centum sexaginta duobus annis, et genuit Henoch.
19 Bayan ya haifi Enok, Yared ya yi shekaru 800, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et vixit Iared, postquam genuit Henoch, octingentis annis, et genuit filios et filias.
20 Gaba ɗaya dai, Yared ya yi shekara 962, sa’an nan ya mutu.
Et facti sunt omnes dies Iared nongenti sexaginta duo anni, et mortuus est.
21 Sa’ad da Enok ya yi shekara 65, sai ya haifi Metusela.
Porro Henoch vixit sexaginta quinque annis, et genuit Mathusalam.
22 Bayan ya haifi Metusela, Enok ya kasance cikin zumunci da Allah shekaru 300, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et ambulavit Henoch cum Deo: et vixit, postquam genuit Mathusalam, trecentis annis, et genuit filios et filias.
23 Gaba ɗaya dai, Enok ya yi shekaru 365.
Et facti sunt omnes dies Henoch trecenti sexaginta quinque anni.
24 Enok ya kasance cikin zumunci da Allah, sa’an nan ba a ƙara ganinsa ba. Saboda Allah ya ɗauke shi.
Ambulavitque cum Deo, et non apparuit: quia tulit eum Deus.
25 Sa’ad da Metusela ya yi shekara 187, sai ya haifi Lamek.
Vixit quoque Mathusala centum octoginta septem annis, et genuit Lamech.
26 Bayan ya haifi Lamek, Metusela ya yi shekaru 782, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
Et vixit Mathusala, postquam genuit Lamech, septingentis octoginta duobus annis, et genuit filios et filias.
27 Gaba ɗaya dai, Metusela ya yi shekaru 969, sa’an nan ya mutu.
Et facti sunt omnes dies Mathusala nongenti sexaginta novem anni, et mortuus est.
28 Sa’ad da Lamek ya yi shekara 182, sai ya haifi ɗa.
Vixit autem Lamech centum octoginta duobus annis, et genuit filium:
29 Ya ba shi suna Nuhu ya kuma ce, “Zai yi mana ta’aziyya a cikin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la’anta.”
vocavitque nomen eius Noe, dicens: Iste consolabitur nos ab operibus et laboribus manuum nostrarum in terra, cui maledixit Dominus.
30 Bayan an haifi Nuhu, Lamek ya yi shekara 595, yana kuma da’ya’ya maza da mata.
Vixitque Lamech, postquam genuit Noe, quingentis nonaginta quinque annis, et genuit filios et filias.
31 Gaba ɗaya dai, Lamek ya yi shekaru 777, sa’an nan ya mutu.
Et facti sunt omnes dies Lamech, septingenti septuaginta septem anni, et mortuus est.
32 Bayan Nuhu ya yi shekara 500, sai ya haifi Shem, Ham da Yafet.
Noe vero cum quingentorum esset annorum, genuit Sem, Cham, et Iapheth.

< Farawa 5 >