< Farawa 36 >

1 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa (wato, Edom).
The following is the genealogy of Esau (also known as Edom).
2 Isuwa ya ɗauko matansa daga cikin matan Kan’ana, ya ɗauko Ada’yar Elon mutumin Hitti, da Oholibama’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon Bahiwiye
Esau married two Canaanite women: Adah, daughter of Elon the Hittite, and Oholibamah, daughter of Anah, and granddaughter of Zibeon the Hivite.
3 ya kuma auri Basemat’yar Ishmayel wadda take’yar’uwar Nebayiwot.
In addition he married Basemath, daughter of Ishmael and sister of Nebaioth.
4 Ada ta haifi wa Isuwa, Elifaz. Basemat kuma ta haifa masa Reyuwel.
Adah had a son for Esau named Eliphaz. Basemath had Reul.
5 Oholibama kuwa ta haifa masa Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza, waɗanda aka haifa masa a Kan’ana.
Oholibamah had Jeush, Jalam, and Korah. These were the sons of Esau, who were born to him in Canaan.
6 Isuwa ya ɗauki matansa da’ya’yansa maza da mata da kuma dukan membobin gidansa, ya kuma ɗauki shanunsa da dukan sauran dabbobinsa, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan’ana zuwa wata ƙasa nesa da ɗan’uwansa Yaƙub.
Esau took his wives, sons and daughters, and everyone in his household, together with his livestock, all his other animals, and all the possessions he had gained while in Canaan, and went to live in a country far away from his brother Jacob.
7 Mallakarsu ta yi yawa ƙwarai da ba za su iya zauna tare ba; gama ƙasar da suke zaune a ciki ba za tă ishe su su biyu ba saboda dabbobinsu.
He did this because the land they were living in couldn't support both of them with all their livestock.
8 Saboda haka Isuwa (wato, Edom) ya zauna a ƙasar tuddai na Seyir.
Esau settled down in the hill country of Seir.
9 Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom, a ƙasar tuddai na Seyir.
The following is the genealogy of Esau, father of the Edomites, who lived in the hill country of Seir:
10 Waɗannan su ne sunayen’ya’yan Isuwa maza, Elifaz, ɗan Ada matar Isuwa, da Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa.
These were the names of Esau's sons: Eliphaz, son of Esau's wife Adah, and Reuel, son of Esau's wife Basemath.
11 ’Ya’yan Elifaz maza su ne, Teman, Omar, Zefo, Gatam da Kenaz.
The sons of Eliphaz were: Teman, Omar, Zepho, Gatam, and Kenaz.
12 Elifaz ɗan Isuwa kuma yana da ƙwarƙwara mai suna Timna, wadda ta haifa masa Amalek. Waɗannan su ne jikokin Ada matar Isuwa.
Timna, the concubine of Esau's son Eliphaz, had Amalek for Eliphaz. These were the descendants of Esau's wife Adah.
13 ’Ya’yan Reyuwel maza su ne, Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
These were the sons of Reuel: Nahath, Zerah, Shammah, and Mizzah. They were the descendants of Esau's wife Basemath.
14 ’Ya’yan Oholibama maza’yar Ana wadda take jikanyar Zibeyon, matar Isuwa, waɗanda ta haifa wa Isuwa su ne, Yewush, Yalam da Kora.
These were the sons of Esau's wife Oholibamah, daughter of Anah and granddaughter of Zibeon, whom she had for Esau: Jeush, Jalam, and Korah.
15 Waɗannan su ne manya a cikin zuriyar Isuwa,’Ya’ya Elifaz maza ɗan farin Isuwa, Shugabannin su ne; Teman, Omar, Zefo, Kenaz,
These were the tribal leaders of Esau's sons. The tribal leaders of the sons of Eliphaz (Esau's firstborn) were Teman, Omar, Zepho, Kenaz,
16 Kora, Gatam da kuma Amalek. Waɗannan ne manya da suka fito daga dangin Elifaz a Edom; su ne jikokin Ada.
Korah, Gatam, and Amalek. They were the tribal leaders of Eliphaz in the country of Edom, and they were the descendants of Adah.
17 ’Ya’yan Reyuwel maza, Shugabannin su ne; Nahat, Zera, Shamma da Mizza. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Reyuwel a Edom; su ne jikokin Basemat matar Isuwa.
These were the sons of Esau's son Reuel: tribal leaders Nahath, Zerah, Shammah, and Mizzah. They were the tribal leaders descended from Reuel in the country of Edom, and they were the descendants of Esau's wife Basemath.
18 ’Ya’yan Oholibama maza matar Isuwa, Shugabannin su ne; Yewush, Yalam da Kora. Waɗannan su ne manya da suka fito daga dangin Oholibama’yar Ana matar Isuwa.
These were the sons of Esau's wife Oholibamah: tribal leaders Jeush, Jalam, and Korah; they were the tribal leaders descended from Esau's wife Oholibamah, daughter of Anah.
19 Waɗannan su ne’ya’yan Isuwa maza (wato, Edom), waɗannan ne manyansu.
All these were the sons of Esau (also called Edom), and they were their tribal leaders.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Seyir Bahore maza, waɗanda suke zaune a yankin, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These were the sons of Seir the Horite, who were living in the country: Lotan, Shobal, Zibeon, Anah,
21 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa,’ya’yan Seyir, maza, a ƙasar Edom.
Dishon, Ezer, and Dishan; they were the tribal leaders of the Horites, the descendants of Seir in the land of Edom.
22 ’Ya’yan Lotan maza su ne, Hori da Homam. Timna’yar’uwar Lotan ce.
The sons of Lotan were Hori and Hemam. Timna was Lotan's sister.
23 ’Ya’yan Shobal maza su ne, Alwan, Manahat, Ebal, Shefo da Onam.
These were the sons of Shobal: Alvan, Manahath, Ebal, Shepho, and Onam.
24 ’Ya’yan Zibeyon maza su ne, Aiya da Ana. Wannan shi ne Ana wanda ya sami maɓulɓulan ruwan zafi a hamada yayinda yake kiwon jakuna na mahaifinsa Zibeyon.
These were the sons of Zibeon: Aiah and Anah. (This was the Anah who discovered the hot springs in the desert while he was looking after the donkeys of his father Zibeon.)
25 ’Ya’yan Ana su ne, Dishon da Oholibama’yar Ana.
These were the children of Anah: Dishon and Oholibamah, daughter of Anah.
26 ’Ya’yan Dishon maza su ne, Hemdan, Eshban, Itran da Keran.
These were the sons of Dishon: Hemdan, Eshban, Ithran, and Cheran.
27 ’Ya’yan Ezer maza su ne, Bilhan, Za’aban da Akan.
These were the sons of Ezer: Bilhan, Zaavan, and Akan.
28 ’Ya’yan Dishan maza su ne, Uz da Aran.
These were the sons of Dishan: Uz and Aran.
29 Waɗannan su ne manyan Horiyawa, Lotan, Shobal, Zibeyon, Ana,
These were the tribal leaders of the Horites: tribal leaders Lotan, Shobal, Zibeon, Anah,
30 Dishon, Ezer da Dishan. Waɗannan su ne manyan Horiyawa, bisa ga ɓangarorinsu, a ƙasar Seyir.
Dishon, Ezer, and Dishan. They were the tribal leaders of the Horites listed according to their tribes in the country of Seir.
31 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi mulki a Edom kafin wani sarki mutumin Isra’ila yă yi mulki,
These were the kings who ruled in the land of Edom before there was any king who ruled over the Israelites:
32 Bela ɗan Beyor ya zama sarkin Edom. Sunan birninsa shi ne Dinhaba.
Bela, son of Beor, ruled in Edom and the name of his town was Dinhabah.
33 Sa’ad da Bela ya rasu, Yobab ɗan Zera daga Bozra ya gāje shi.
When Bela died, Jobab, son of Zerah from Bozrah, took over as king.
34 Sa’ad da Yobab ya rasu, Husham daga ƙasar Temaniyawa ya gāje shi.
When Jobab died, Husham from the land of the Temanites took over as king.
35 Sa’ad da Husham ya rasu, Hadad ɗan Bedad, wanda ya ci Midiyan da yaƙi a ƙasar Mowab, ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Awit.
When Husham died, Hadad, son of Bedad, took over as king. He was the one who defeated the Midianites in the country of Moab, and the name of his town was Avith.
36 Sa’ad da Hadad ya rasu, Samla daga Masreka ya gāje shi.
When Hadad died, Samlah from Masrekah took over as king.
37 Sa’ad da Samla ya rasu, Sha’ul daga Rehobot na ta kogi ya gāje shi.
When Samlah died, Shaul from Rehoboth on the Euphrates took over as king.
38 Sa’ad da Sha’ul ya rasu, Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya gāje shi.
When Shaul died, Baal-hanan, son of Achbor, took over as king.
39 Sa’ad da Ba’al-Hanan ɗan Akbor ya rasu, Hadad ya gāje shi. Sunan birninsa shi ne Fau, kuma sunan matarsa Mehetabel ce’yar Matired, jikanyar Me-Zahab.
When Baal-hanan, son of Achbor, died, Hadad took over as king. The name of his town was Pau, and his wife's name was Mehetabel, daughter of Matred, daughter of Me-zahab.
40 Waɗannan su ne manya da suka fito daga zuriyar Isuwa, bisa ga danginsu, bisa kuma ga kabilansu da yankunansu. Sunayensu su ne, Timna, Alwa, Yetet.
These were the names of the tribal leaders descended from Esau, according to their families and where they lived, listed by name: tribal leaders Timna, Alvah, Jetheth,
41 Oholibama, Ela, Finon.
Oholibamah, Elah, Pinon,
42 Kenaz, Teman, Mibzar.
Kenaz, Teman, Mibzar,
43 Magdiyel da Iram. Waɗannan su ne manyan Edom bisa ga mazauninsu cikin ƙasar da suka zauna. Wannan shi ne zuriyar Isuwa, kakan mutanen Edom.
Magdiel, and Iram. These were the tribal leaders of Edom, listed according to the places where they lived in the country. Esau was the ancestor of the Edomites.

< Farawa 36 >