< Farawa 34 >

1 To, Dina,’yar da Liyatu ta haifa wa Yaƙub, ta je ta ziyarci matan ƙasar.
And Dinah the daughter of Leah, whom she had borne unto Jacob, went out to see the daughters of the land.
2 Sa’ad da Shekem ɗan Hamor Bahiwiye mai mulkin wurin ya gan ta, sai ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta.
And Shechem the son of Hamor the Hivite, the prince of the land, saw her; and he took her, and lay with her, and humbled her.
3 Zuciyarsa kuwa ta damu da son Dina’yar Yaƙub, ya kuwa ƙaunaci yarinyar, ya yi mata magana a hankali.
And his soul did cleave unto Dinah the daughter of Jacob, and he loved the damsel, and spoke comfortingly unto the damsel.
4 Sai Shekem ya ce wa mahaifinsa Hamor, “Ka auro mini wannan yarinya ta zama matata.”
And Shechem spoke unto his father Hamor, saying: 'Get me this damsel to wife.'
5 Sa’ad da Yaƙub ya ji cewa an ɓata’yarsa Dina, sai ya yi shiru game da batun sai’ya’yansa maza sun dawo gida, gama’ya’yansa suna a jeji tare da dabbobinsa suna kiwo.
Now Jacob heard that he had defiled Dinah his daughter; and his sons were with his cattle in the field; and Jacob held his peace until they came.
6 Sai Hamor mahaifin Shekem ya je don yă yi magana da Yaƙub.
And Hamor the father of Shechem went out unto Jacob to speak with him.
7 Da’ya’yan Yaƙub maza suka dawo daga jeji sai suka ji labarin. Abin kuwa ya zafe su ƙwarai, don Shekem ya jawo abin kunya wa jama’ar Isra’ila ta wurin kwana da’yar Yaƙub, don bai kamata wannan abu yă faru ba.
And the sons of Jacob came in from the field when they heard it; and the men were grieved, and they were very wroth, because he had wrought a vile deed in Israel in lying with Jacob's daughter; which thing ought not to be done.
8 Amma Hamor ya ce musu, “Ɗana Shekem ya sa zuciyarsa a kan’yarku. Ina roƙonku ku ba shi ita yă aura.
And Hamor spoke with them, saying 'The soul of my son Shechem longeth for your daughter. I pray you give her unto him to wife.
9 Ku yi auratayya da mu; ku aurar mana da’ya’yanku mata, ku kuma ku auro’ya’yanmu mata wa kanku.
And make ye marriages with us; give your daughters unto us, and take our daughters unto you.
10 Za ku iya zauna a cikinmu, ƙasar tana nan a buɗe dominku. Ku yi zama a cikinta, ku yi sana’a, ku kuma sami dukiya.”
And ye shall dwell with us; and the land shall be before you; dwell and trade ye therein, and get you possessions therein.'
11 Sai Shekem ya ce wa mahaifin Dina da kuma’yan’uwanta. “Bari in sami tagomashi a idanunku, zan kuwa ba ku duk abin da kuka tambaya.
And Shechem said unto her father and unto her brethren: 'Let me find favour in your eyes, and what ye shall say unto me I will give.
12 Ku faɗa mini nawa ne dukiyar aure da kuma sadakin da zan kawo bisa ga yadda kuke so, zan kuwa biya duk abin da kuka ce. Ku dai bar ni in aure yarinyar ta zama matata.”
Ask me never so much dowry and gift, and I will give according as ye shall say unto me; but give me the damsel to wife.'
13 Domin an ɓata’yar’uwansu Dina, sai’ya’yan Yaƙub maza suka amsa a ha’ince yayinda suke wa Shekem da mahaifinsa Hamor magana.
And the sons of Jacob answered Shechem and Hamor his father with guile, and spoke, because he had defiled Dinah their sister,
14 Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, ba za mu iya ba da’yar’uwarmu ga mutumin da ba shi da kaciya ba. Wannan zai zama abin kunya ne a gare mu.
and said unto them: 'We cannot do this thing, to give our sister to one that is uncircumcised; for that were a reproach unto us.
15 Za mu yarda da wannan kaɗai ta wannan sharaɗi, cewa za ku zama kamar mu ta wurin yin wa dukan’ya’yanku maza kaciya.
Only on this condition will we consent unto you: if ye will be as we are, that every male of you be circumcised;
16 Sa’an nan za mu ba da’ya’yanmu mata aure gare ku, mu kuma mu aure’ya’yanku mata wa kanmu. Za mu zauna a cikinku mu kuma zama mutane ɗaya da ku.
then will we give our daughters unto you, and we will take your daughters to us, and we will dwell with you, and we will become one people.
17 Amma in ba za ku yarda a yi muku kaciya ba, za mu ɗauki’yar’uwanmu mu tafi.”
But if ye will not hearken unto us, to be circumcised; then will we take our daughter, and we will be gone.'
18 Sharuɗansu sun gamshi Hamor da ɗansa, Shekem.
And their words pleased Hamor, and Shechem Hamor's son.
19 Saurayin wanda aka fi girmamawa a cikin dukan gidan mahaifinsa, bai ɓata lokaci a yin abin da suka ce ba, domin ya ji daɗin’yar Yaƙub.
And the young man deferred not to do the thing, because he had delight in Jacob's daughter. And he was honoured above all the house of his father.
20 Saboda haka Hamor da ɗansa Shekem suka tafi ƙofar birninsu don su yi magana da mutanen garinsu.
And Hamor and Shechem his son came unto the gate of their city, and spoke with the men of their city, saying:
21 Suka ce, “Waɗannan mutane ba su da damuwa, bari su zauna a cikin ƙasarmu, su kuma yi sana’a a ciki; ƙasar tana da isashen fili dominsu. Za mu iya auro’ya’yansu mata, su kuma su auri namu.
'These men are peaceable with us; therefore let them dwell in the land, and trade therein; for, behold, the land is large enough for them; let us take their daughters to us for wives, and let us give them our daughters.
22 Amma mutanen za su yarda su zauna tare da mu kamar mutane ɗaya kawai bisa wannan sharaɗi, cewa a yi wa mazanmu kaciya, kamar yadda su kansu suke.
Only on this condition will the men consent unto us to dwell with us, to become one people, if every male among us be circumcised, as they are circumcised.
23 Ashe, shanunsu, dukiyarsu da dukan sauran dabbobinsu, ba za su zama namu ba? Saboda haka mu yarda, za su kuwa zauna a cikinmu.”
Shall not their cattle and their substance and all their beasts be ours? only let us consent unto them, and they will dwell with us.'
24 Dukan mazan da suka fito ƙofar birnin suka yarda da Hamor da kuma ɗansa Shekem, aka kuwa yi wa kowane namiji a birnin kaciya.
And unto Hamor and unto Shechem his son hearkened all that went out of the gate of his city; and every male was circumcised, all that went out of the gate of his city.
25 Bayan kwana uku, yayinda dukansu suna cikin zafi mikin kaciya, sai biyu daga cikin’ya’yan Yaƙub maza, Simeyon da Lawi,’yan’uwan Dina, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka kashe kowane namiji.
And it came to pass on the third day, when they were in pain, that two of the sons of Jacob, Simeon and Levi, Dinah's brethren, took each man his sword, and came upon the city unawares, and slew all the males.
26 Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dina daga gidan Shekem suka tafi.
And they slew Hamor and Shechem his son with the edge of the sword, and took Dinah out of Shechem's house, and went forth.
27 Sa’an nan’ya’yan Yaƙub maza suka bi kan gawawwakin, suka washe arzikin birni saboda an ɓata’yar’uwarsu.
The sons of Jacob came upon the slain, and spoiled the city, because they had defiled their sister.
28 Suka kwashe garkunansu na shanu da jakuna, da kuma kome na mutanen a birnin da kuma cikin gonaki.
They took their flocks and their herds and their asses, and that which was in the city and that which was in the field;
29 Suka kwashe dukan dukiyarsu da dukan matansu da’ya’yansu, suka kwashe kome da yake cikin gidaje.
and all their wealth, and all their little ones and their wives, took they captive and spoiled, even all that was in the house.
30 Sai Yaƙub ya ce wa Simeyon da Lawi, “Kun jawo mini wahala ta wurin sa in zama abin ƙi ga Kan’aniyawa da Ferizziyawa, mazaunan wannan ƙasa. Mu kima ne, in kuwa suka haɗa kai gāba da ni, suka fāɗa mini, za su hallaka ni da gidana.”
And Jacob said to Simeon and Levi: 'Ye have troubled me, to make me odious unto the inhabitants of the land, even unto the Canaanites and the Perizzites; and, I being few in number, they will gather themselves together against me and smite me; and I shall be destroyed, I and my house.'
31 Amma’ya’yansa suka amsa, “To, ya dace ke nan da ya yi da’yar’uwarmu kamar karuwa?”
And they said: 'Should one deal with our sister as with a harlot?'

< Farawa 34 >