< Farawa 31 >

1 Yaƙub ya ji cewa’ya’ya Laban mazan suna cewa, “Yaƙub ya kwashe dukan abin da mahaifinmu yake da shi, ya kuma sami dukan wannan arziki daga abin da yake na mahaifinmu.”
He heard the words of Laban's sons, saying, "Jacob has taken away all that was our father's. From that which was our father's he has gained all this wealth."
2 Yaƙub kuma ya lura cewa halin Laban gare shi ya canja ba kamar yadda yake a dā ba.
Jacob saw the expression on Laban's face, and look, it was not as it had been.
3 Sai Ubangiji ya ce wa Yaƙub, “Koma ƙasar kakanninka da kuma danginka, zan kuwa kasance tare da kai.”
Then God said to Jacob, "Return to the land of your fathers, and to your relatives, and I will be with you."
4 Saboda haka Yaƙub ya aika a ce wa Rahila da Liyatu su zo jeji inda garkunan suke.
Jacob sent and called Rachel and Leah to the field where his flock was,
5 Sai ya ce musu, “Na ga cewa halin mahaifinku gare ni ba kamar yadda dā yake ba, amma Allah na mahaifina yana tare da ni.
and said to them, "I see the expression on your father's face, that it is not what it was before. But the God of my father has been with me.
6 Kun san cewa na yi aiki wa mahaifinku da dukan ƙarfina,
You know that I have served your father with all of my strength.
7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni ta wurin sauya albashina sau goma. Amma dai, Allah bai yardar masa yă yi mini lahani ba.
Yet your father has cheated me and changed my wages ten times, but God did not allow him to hurt me.
8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce, ‘Masu zāne-zāne ne za su zama ladanka,’ sai dukan garkunan su haifi ƙananan masu zāne-zāne.
If he said this, 'The speckled will be your wages,' then all the flock bore speckled. If he said this, 'The streaked will be your wages,' then all the flock bore streaked.
9 Ta haka Allah ya kwashe dabbobin mahaifinku ya ba ni.
Thus God has taken away your father's livestock and given them to me.
10 “A lokacin ɗaukar cikin garken, na taɓa yin mafarki inda na ga bunsuran da suke barbara da garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne.
And it came about at the time when the flocks were breeding I looked up and saw in a dream, and look, the male goats which leaped on the flock were streaked, speckled, and spotted.
11 Sai mala’ikan Allah ya ce mini a mafarkin, ‘Yaƙub.’ Sai na amsa na ce, ‘Ga ni.’
The angel of God said to me in the dream, 'Jacob,' and I said, 'Here I am.'
12 Ya ce, ‘Ɗaga idanunka ka gani, dukan bunsuran da suke hawan garken, masu dabbare-dabbare, ko babare-babare, ko masu zāne-zāne ne, gama na ga dukan abin da Laban yake yin maka.
He said, 'Now lift up your eyes, and look, all the male goats which leap on the flock are streaked, speckled, and spotted, for I have seen all that Laban has done to you.
13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa al’amudi mai, da kuma inda ka yi mini alkawari. Yanzu ka bar wannan ƙasa nan take, ka koma ƙasarka ta ainihi.’”
I am the God of Bethel, where you anointed a standing-stone, where you made a vow to me. Now arise, go out from this land and return to the land of your birth.'"
14 Sai Rahila da Liyatu suka amsa suka ce, “Muna da wani rabo a gādon kayan mahaifinmu ne?
Rachel and Leah answered him, "Is there yet any portion or inheritance for us in our father's house?
15 Ba kamar baƙi ne yake ɗaukarmu ba? Ba sayar da mu kaɗai ya yi ba, har ma ya yi amfani da abin da aka biya saboda mu.
Aren't we regarded by him as foreigners? For he has sold us, and he has used up what was paid for us.
16 Tabbatacce dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga mahaifinmu ya zama namu da’ya’yanmu. Saboda haka ka yi duk abin da Allah ya faɗa maka.”
For all the wealth which God has taken away from our father, that is ours and our children's. Now then, whatever God has said to you, do."
17 Sa’an nan Yaƙub ya sa’ya’yansa da matansa a kan raƙuma,
Then Jacob got up and put his sons and his wives on the camels,
18 ya kuma kora dukan dabbobinsa, suka ja gabansa, tare da dukan abubuwan da ya samu a Faddan Aram, don su tafi wurin mahaifinsa Ishaku a ƙasar Kan’ana.
and he took away all his livestock and all his property which he had acquired, including the livestock which he had gained in Paddan Aram, to go to Isaac his father in the land of Canaan.
19 Sa’ad da Laban ya tafi don askin tumakinsa, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta.
Now Laban had gone to shear his sheep, and Rachel stole the idols that belonged to her father.
20 Yaƙub kuwa ya ruɗe Laban mutumin Aram da bai sanar da shi zai gudu ba.
Jacob outwitted Laban the Aramean by not telling him that he intended to flee.
21 Saboda haka ya gudu da dukan abin da ya mallaka, ya ƙetare Kogi, ya nufi yankin tuddan Gileyad.
So he fled with everything that he had, and he arose and crossed the River, and set out toward the hill country of Gilead.
22 A rana ta uku, sai aka faɗa wa Laban cewa Yaƙub ya gudu.
Laban was told on the third day that Jacob had fled.
23 Sai Laban ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi bayan Yaƙub har kwana bakwai, ya kuma same shi a yankin tuddan Gileyad.
He took his relatives with him, and pursued after him for seven days, and caught up with him in the hill country of Gilead.
24 Sai Allah ya bayyana ga Laban mutumin Aram a mafarki da dare, ya ce masa, “Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu, ko mai kyau ko marar kyau.”
God came to Laban the Aramean in a dream at night, and said to him, "Be careful that you do not speak to Jacob either good or bad."
25 Yaƙub ya riga ya kafa tentinsa a yankin tuddan Gileyad sa’ad da Laban ya same shi. Laban da danginsa suka kafa sansani a can su ma.
Laban caught up with Jacob. Now Jacob had pitched his tent in the hill country, and Laban with his relatives camped in the hill country of Gilead.
26 Sai Laban ya ce wa Yaƙub, “Me ke nan ka yi? Ka ruɗe ni, ka kuma ɗauki’ya’yana mata kamar kamammun yaƙi.
Laban said to Jacob, "What have you done? You have deceived me, and carried away my daughters like captives taken in war?
27 Me ya sa ka gudu a ɓoye ka kuma ruɗe ni? Me ya sa ba ka faɗa mini don in sallame ka da farin ciki da waƙoƙi haɗe da kiɗin ganguna da garayu ba?
Why did you flee in secret and deceive me, and not tell me, so that I might have sent you away with joy and singing, with a tambourine and with a lyre.
28 Ba ka ma bari in sumbaci jikokina da’ya’yana mata in yi musu bankwana ba. Ka yi wauta.
And you did not allow me to kiss my sons and my daughters? Now you have done foolishly.
29 Ina da iko in cuce ka; amma jiya da dare Allahn mahaifinka ya faɗa mini, ‘Ka yi hankali kada ka faɗa wa Yaƙub wani abu ko mai kyau ko marar kyau.’
It is in my power to do you harm, but the God of your father spoke to me last night, saying, 'Be careful that you do not speak to Jacob either good or bad.'
30 Yanzu ka gudu domin kana marmari komawa gidan mahaifinka. Amma don me ka sace mini gumakana?”
Now you have indeed gone away, because you longed greatly for your father's house. But why have you stolen my gods?"
31 Yaƙub ya amsa wa Laban, “Na ji tsoro ne, domin na yi tsammani za ka ƙwace’ya’yanka mata daga gare ni ƙarfi da yaji.
Jacob answered Laban, "Because I was afraid, for I thought that you would take your daughters from me by force.'
32 Amma in ka sami wani wanda yake da gumakanka, ba zai rayu ba. Kai da kanka ka duba a gaban danginmu, ko akwai wani abin da yake naka a nan tare da ni; in ka gani, ka ɗauka.” Yaƙub dai bai san cewa Rahila ta sace gumakan ba.
Anyone you find your gods with shall not live. In the presence of our relatives, identify what I have that is yours, and take it with you." For Jacob did not know that Rachel had stolen them.
33 Saboda haka Laban ya shiga tentin Yaƙub, ya shiga tentin Liyatu da kuma tentuna matan nan biyu bayi, amma bai sami kome ba. Bayan ya fita daga tentin Liyatu, sai ya shiga tentin Rahila.
Laban went into Jacob's tent, into Leah's tent, and into the tent of the two female servants; but he did not find them. He went out of Leah's tent, and entered into Rachel's tent.
34 Rahila fa ta kwashe gumakan gidan ta sa su cikin sirdin raƙumi, ta kuma zauna a kansu. Laban ya bincika cikin kowane abu a tentin amma bai sami kome ba.
Now Rachel had taken the idols, put them in the camel's saddle, and sat on them. Laban searched the whole tent, but did not find them.
35 Sai Rahila ta ce wa mahaifinta, “Kada ka yi fushi, ranka yă daɗe da ban tashi tsaye a gabanka ba; gama ina al’adar mata ne.” Saboda haka ya bincika amma bai sami gumakan gidan ba.
She said to her father, "Do not let my lord be angry that I can't rise up before you; for the manner of women is on me." He searched, but did not find the teraphim.
36 Yaƙub ya fusata, ya kuma yi wa Laban faɗa. Ya tambayi Laban, “Mene ne laifina? Wanda zunubi na yi da kake farautata?
Jacob was angry, and argued with Laban. Jacob answered Laban, "What is my trespass? What is my sin, that you have hotly pursued after me?
37 Yanzu da ka bincika dukan kayayyakina, me ka samu da yake na gidanka? Kawo shi nan a gaban danginka da kuma dangina, bari su zama alƙali tsakaninmu biyu.
Now that you have searched around in all my stuff, did you find anything from all of your household's belongings? Put it here before my relatives and your relatives, that they may judge between the two of us.
38 “Na kasance tare da kai shekaru ashirin. Tumakinka da awakinka ba su yi ɓarin ciki ba, ban kuwa ci raguna daga garkunanka ba.
These twenty years I have been with you. Your ewes and your female goats have not miscarried their young, and I haven't eaten the rams of your flocks.
39 Ban kawo dabbobinka da namun jeji suka yayyaga; na kuma ɗauki hasarar ba? Ka nemi in biya dukan abin da aka sace da rana ko da dare.
That which was torn by animals I did not bring to you. I bore its loss. You demanded payment from me whether stolen by day or stolen by night.
40 Yanayin da na kasance ke nan, da rana na sha zafin rana da dare kuma na sha sanyi, ga rashin barci.
I was consumed by the heat during the day and by the frost at night, and sleepless nights.
41 Haka ya kasance shekaru ashirin da na yi a gidanka. Na yi maka aiki shekaru goma sha huɗu domin’ya’yanka mata biyu, na kuma yi shekaru shida domin garkunanka, ka kuma canja albashina sau goma.
These twenty years I have been in your house. I served you fourteen years for your two daughters, and six years for your flock, and you have changed my wages ten times.
42 Da ba don Allah na mahaifina, Allah na Ibrahim da kuma Tsoron Ishaku ya kasance tare da ni ba, tabbatacce da ka sallame ni hannu wofi. Amma Allah ya ga wahalata da famar hannuwana, ya kuwa tsawata maka da dare jiya.”
Unless the God of my father, the God of Abraham, and the one whom Isaac fears, had been with me, surely now you would have sent me away empty-handed. God has seen my harsh treatment and my hard work, and rebuked you last night."
43 Laban ya amsa wa Yaƙub, “Matan,’ya’yana ne,’ya’yansu,’ya’yana ne, garkunan kuma garkunana ne. Dukan abin da kake gani, nawa ne. Duk da haka me zan yi a rana ta yau ga waɗannan’ya’yana mata, ko kuma ga’ya’yan da suka haifa?
Laban answered Jacob, "The daughters are my daughters, the children are my children, the flocks are my flocks, and all that you see is mine: and what can I do this day to these my daughters, or to their children whom they have borne?
44 Zo, bari mu ƙulla yarjejjeniya, da kai da ni, bari kuma ta kasance shaida a tsakaninmu.”
So now, come, let us make a covenant, you and I, and let it be a witness between the two of us." And he said to him, "Look, there is no one with us; see, God is witness between me and you."
45 Saboda haka Yaƙub ya ɗauki dutse ya kafa yă zama al’amudi.
Jacob took a stone and set it up as a standing-stone.
46 Ya ce wa danginsa. “Ku tattara waɗansu duwatsu.” Sai suka kwashe duwatsu suka tsiba, suka kuwa ci abinci a can kusa da tsibin.
Jacob said to his relatives, "Gather stones." So they took stones and made a mound. They ate there by the mound.
47 Laban ya sa masa suna Yegar Sahaduta, Yaƙub kuwa ya kira shi Galeyed.
Laban called it Jegar Sahadutha, but Jacob called it Galeed.
48 Laban ya ce, “Wannan tsibi, shi ne shaida tsakaninka da ni a yau.” Shi ya sa aka kira shi Galeyed.
Laban said, "This mound is a witness between me and you today." Therefore it was named Galeed
49 Aka kuma kira shi Mizfa, domin ya ce, “Ubangiji yă sa ido tsakanin ni da kai sa’ad da muka rabu da juna.
and Mizpah, for he said, "God watch between me and you, when we are absent one from another.
50 Laban ya ce in ka wulaƙanta’ya’yana mata, ko ka auri waɗansu mata ban da’ya’yana mata, ko da yake babu wani da yake tare da mu, ka tuna cewa Allah shi ne shaida tsakaninka da ni.”
If you mistreat my daughters, or if you take wives besides my daughters, although no one is with us; see, God is witness between me and you."
51 Laban ya kuma ce wa Yaƙub, “Ga wannan tsibi, ga kuma wannan al’amudin da na kafa tsakaninka da ni.
Laban said to Jacob, "See this mound, and see the standing-stone, which I have set between me and you.
52 Wannan tsibin shi ne shaida, wannan al’amudi kuma shaida ne, cewa ba zan tsallake wannan tsibi zuwa gefenka don in cuce ka ba, kai kuma ba za ka tsallake wannan tsibi da al’amudi zuwa gefena don ka cuce ni ba.
May this mound be a witness, and the standing-stone be a witness, that I will not pass over this mound to you, and that you will not pass over this mound and this standing-stone to me, to do harm.
53 Bari Allah na Ibrahim da Allah na Nahor, Allah na iyayensu, yă zama alƙali tsakaninmu.” Saboda haka Yaƙub ya yi rantsuwa da sunan Tsoron mahaifinsa Ishaku.
The God of Abraham, and the God of Nahor, judge between us." Then Jacob swore by the fear of his father Isaac.
54 Ya miƙa hadaya a can a ƙasar tudu, ya kuma gayyaci danginsa zuwa wurin cin abinci. Bayan suka ci, sai suka kwana a can.
Jacob offered a sacrifice on the mountain, and called his relatives to eat the meal. They ate the meal and stayed all night on the mountain.
55 Da sassafe kashegari sai Laban ya sumbaci jikokinsa da’ya’yansa mata, ya sa musu albarka. Sa’an nan ya yi bankwana da su, ya koma gida.
Early in the morning, Laban rose up, and kissed his sons and his daughters, and blessed them. Laban departed and returned to his place.

< Farawa 31 >