< Farawa 30 >

1 Sa’ad da Rahila ta ga cewa ba tă haifa wa Yaƙub’ya’ya ba, sai ta fara kishin’yar’uwarta. Saboda haka ta ce wa Yaƙub, “Ka ba ni’ya’ya, ko kuwa in mutu!”
When Rahel sawe that she bare Iacob no childern she enuied hir sister and sayde vnto Iacob: geue me childern or ells I am but deed.
2 Yaƙub ya fusata da ita ya ce, “Ina a matsayin Allah ne wanda ya hana ke samun’ya’ya?”
Than was Iacob wrooth with Rahel saynge: Am I in godes steade which kepeth fro the the frute of thi wobe?
3 Sa’an nan ta ce, “Ga Bilha, mai baiwata, ka kwana da ita don tă haifa mini’ya’ya, ta gare ta kuwa ni ma in gina iyali.”
The she sayde: here is my mayde Bilha: go in vnto her that she maye beare vpo my lappe that I maye be encreased by her.
4 Saboda haka ta ba shi baranyarta Bilha tă zama matarsa. Yaƙub kuwa ya kwana da ita,
And she gaue him Bilha hir hadmayde to wife. And Iacob wet in vnto her
5 ta kuwa yi ciki, ta kuma haifi ɗa.
And Bilha conceaued and bare Iacob a sonne.
6 Sa’an nan Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni; ya saurari roƙona ya kuma ba ni ɗa.” Saboda wannan ta ba shi suna Dan.
Than sayde Rahel. God hath geuen sentece on my syde and hath also herde my voyce and hath geuen me a sonne. Therfore called she him Dan.
7 Baranyar Rahila ta sāke yin ciki ta kuma haifi wa Yaƙub ɗa na biyu.
And Bilha Rahels mayde coceaued agayne and bare Iacob a nother sonne.
8 Sai Rahila ta ce, “Na yi kokawa sosai da’yar’uwata, na kuwa yi nasara.” Saboda haka ta kira shi Naftali.
And Rahel sayde. God is turned and I haue made achaunge with my sister and haue gote ye vpper hade. And she called his name Nepthali
9 Sa’ad da Liyatu ta ga cewa ta daina haihuwa, sai ta ɗauki mai hidimarta Zilfa ta ba da ita ga Yaƙub tă zama matarsa.
Whe Lea sawe that she had left bearinge she toke Silpha hir mayde and gaue her Iacob to wiffe.
10 Baranyar Liyatu, Zilfa ta haifa wa Yaƙub ɗa.
And Silpha Leas made bare Iacob a sonne.
11 Sai Liyatu ta ce, “Na yi sa’a!” Saboda haka ta ba shi suna Gad.
Than sayde Lea: good lucke: and called his name Gad.
12 Zilfa baranyar Liyatu ta haifa wa Yaƙub ɗa na biyu.
And Silpha Leas mayde bare Iacob another sonne.
13 Sai Liyatu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Mata za su ce da ni mai farin ciki.” Saboda haka ta sa masa suna Asher.
Tha sayd Lea: happy am I for the doughters will call me blessed. And called his name Asser.
14 A lokacin girbin alkama, sai Ruben ya je jeji ya ɗebo manta-uwa ya kawo wa mahaifiyarsa Liyatu. Sai Rahila ta ce wa Liyatu, “Ina roƙonki ki ɗan sam mini manta-uwa ɗanki.”
And Rube wet out in the wheat haruest and foude mandragoras in the feldes and brought the vnto his mother Lea. Than sayde Rahel to Lea geue me of thy sonnes madragoras.
15 Amma ta ce mata, “Bai ishe ki ba ne da kika ƙwace mijina? Yanzu kuma kina so ki ƙwace manta-uwa na yarona?” Sai Rahila ta ce “Shi ke nan, mijina zai iya kwana da ke yau saboda manta-uwa na ɗanki.”
And Lea answered: is it not ynough yt thou hast take awaye my housbode but woldest take awaye my sonnes mandragoras also? Than sayde Rahel well let him slepe with the this nyghte for thy sonnes mandragoras.
16 Saboda haka sa’ad da Yaƙub ya dawo daga jeji a wannan yamma sai Liyatu ta fito ta tarye shi. Ta ce, “Dole ka kwana da ni, na yi hayarka da manta-uwa na ɗana.” Saboda haka ya kwana da ita a wannan dare.
And whe Iacob came from the feldes at euen Lea went out to mete him and sayde: come into me for I haue bought the with my sonnes mandragoras. And he slepte with her that nyghte.
17 Allah ya saurari Liyatu, ta kuwa yi ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na biyar.
And God herde Lea yt she coceaued and bare vnto Iacob yt. v. sonne.
18 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya sāka mini saboda na ba da mai hidimata ga mijina.” Saboda haka ta ba shi suna Issakar.
Than sayde Lea. God hath geue me my rewarde because I gaue my mayde to my housbod and she called him Isachar.
19 Liyatu ta sāke yin ciki ta kuma haifa wa Yaƙub ɗa na shida.
And Lea coceaued yet agayne and bare Iacob the sexte sonne.
20 Sai Liyatu ta ce, “Allah ya ba ni kyauta mai daraja. A wannan lokaci mijina zai darajarta ni, domin na haifa masa’ya’ya maza shida.” Saboda haka ta ba shi suna Zebulun.
Than sayde she: God hath endewed me with a good dowry. Now will my housbond dwell with me because I haue borne him. vi. sonnes: and called his name Zabulo.
21 Daga baya ta haifi’ya ta kuwa ba ta suna Dina.
After that she bare a doughter and called her Dina.
22 Sai Allah ya tuna da Rahila; ya saurare ta ya kuma buɗe mahaifarta.
And God remebred Rahel herde her and made her frutefull:
23 Sai ta yi ciki ta kuma haifi ɗa ta ce, “Allah ya ɗauke mini kunyata.”
so that she coceaued and bare a sonne and sayde God hath take awaye my rebuke.
24 Ta ba shi suna Yusuf, ta kuma ce, “Bari Ubangiji yă ƙara mini wani ɗa.”
And she called his name Ioseph saynge The lorde geue me yet a nother sonne.
25 Bayan Rahila ta haifi Yusuf, sai Yaƙub ya ce wa Laban, “Ka sallame ni don in koma ƙasata.
As soone as Rahel had borne Ioseph Iacob sayde to Laban: Sede me awaye yt I maye goo vnto myne awne place and cutre
26 Ba ni matana da’ya’yana, waɗanda na bauta maka dominsu, zan kuwa tafi. Ka dai san yadda na bauta maka.”
geue me my wives and my childern for whome I haue serued the and let me goo; for thou knowest what seruyce I haue done the.
27 Amma Laban ya ce masa, “In na sami tagomashi daga gare ka, ina roƙonka ka zauna. Na gane ta wurin duba cewaUbangiji ya albarkace ni saboda kai.”
Than sayde Laban vnto hi: If I haue fownde fauoure in thy syghte (for I suppose yt the LORde hath blessed me for thy sake)
28 Ya ƙara da cewa, “Faɗa albashinka, zan kuwa biya shi.”
appoynte what thy rewarde shalbe and I will geue it ye.
29 Yaƙub ya ce masa, “Ka dai san yadda na yi maka aiki da kuma yadda dabbobinka suka yi yawa a hannuna.
But he sayde vnto hym thou knowest what seruyce I haue done ye and in what takynge thy catell haue bene vnder me:
30 Kaɗan da kake da shi kafin zuwata ya ƙaru sosai, kuma Ubangiji ya albarkace ka a duk inda na tafi. Amma yanzu, yaushe zan yi wani abu domin gidana ni ma?”
for it was but litle that thou haddest before I came and now it is encreased in to a multitude and the LORDE hath blessed the for my sake. But now when shall I make provysion for myne awne house also?
31 Sai Laban ya yi tambaya, “Me zan ba ka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Kada ka ba ni wani abu. Amma in za ka yi mini abu guda ɗaya, zan ci gaba da kiwon garkunanka, ina kuma lura da su.
And he sayde: what shall I geue the? And Iacob answerd: thou shalt geue me nothinge at all yf thou wilt do this one thinge for me: And then will I turne agayne and fede thy shepe and kepe them.
32 Bari in ratsa cikin dukan garkunanka yau in fid da masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki daga ciki, waɗannan ne za su zama ladana.
I will go aboute all thy shepe this daye and separate fro the all the shepe that are spotted and of dyverse coloures and all blacke shepe amonge the lambes and the partie and spotted amonge the kyddes: And then such shalbe my rewarde.
33 Gaskiyata kuwa za tă zama mini shaida nan gaba, duk sa’ad da ka bincika a kan albashin da ka biya ni. Duk akuyar da take tawa da ba dabbare-dabbare ko babare-babare, ko ɗan ragon da ba baƙi ba, zai kasance sata na yi.”
So shall my rightwesnes answere for me: when the tyme commeth that I shall receaue my rewarde of the: So that what soeuer is not speckeld and partie amonge the gootes and blacke amonge the lambes let that be theft with me.
34 Sai Laban ya ce, “Na yarda. Bari yă zama yadda ka faɗa.”
Than sayde Laban: loo I am contete that it be acordinge as thou hast sayde.
35 A wannan rana ya ware dukan bunsurai da suke dabbare-dabbare da masu zāne-zāne, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare (duka da suke da fari-fari a jikinsu), da dukan baƙaƙen tumaki, ya sa su a hannun’ya’yansa maza.
And he toke out that same daye the he gootes that were partie and of dyuerse coloures and all the she gootes that were spotted and partie coloured and all that had whyte in the and all the blacke amonge the lambes: ad put the in the kepinge of his sonnes
36 Sa’an nan ya sa nisan tafiya kwana uku tsakaninsa da Yaƙub, yayinda Yaƙub ya ci gaba da lura da sauran garkunan Laban Yaƙub.
and sett thre dayes ourney ibetwixte hiselfe and Iacob. And so Iacob kepte ye rest of Labas shepe.
37 Yaƙub ya samo ɗanyen reshen itatuwan aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bar fararen cikin katakon rassan.
Iacob toke roddes of grene popular hasell and of chestnottrees and pilled whyte strakes in the and made the white apere in the staues:
38 Sa’an nan ya zuba ɓararre rassan cikin dukan kwamame na banruwa saboda su kasance a gaban garkunan sa’ad da suka zo shan ruwa. A sa’ad da garkunan suke barbara suka kuma zo shan ruwa,
And he put the staues which he had pilled eue before ye shepe in the gutters and watrynge troughes whe the shepe came to drynke: yt they shulde coceaue whe they came to drynke.
39 sai su yi barbara a gaban rassan. Sai kuwa su haifi ƙanana masu zāne dabbare-dabbare, ko babare-babare ko masu zāne-zāne.
And the shepe coceaued before the staues and brought forth straked spotted and partie.
40 Sai Yaƙub yă ware ƙananan garken dabam, amma sai yă sa sauran su fuskanci dabbobin da suke dabbare-dabbare da kuma baƙaƙe da suke na Laban. Ta haka ya ware garkuna dabam domin kansa bai kuwa haɗa su da dabbobin Laban ba.
The Iacob parted the labes and turned the faces of the shepe toward spotted thinges and toward all maner of blacke thinges thorow out the flockes of Laba. And he made him flockes of his owne by the selfe which he put not vnto the flockes of Laba.
41 A duk sa’ad da ƙarfafa dabbobi mata suke barbara, Yaƙub yakan zuba rassan a kwamame a gaban dabbobin saboda su yi barbara kusa da rassan,
And allwaye in the first buckinge tyme of the shepe Iacob put the staues before the shepe in the gutters yt they myghte conceaue before the staues
42 amma in dabbobin raunana ne, ba ya sa su a can. Saboda haka raunanan dabbobi suka zama na Laban, ƙarfafan kuma suka zama na Yaƙub.
But in the latter buckynge tyme he put them not there: so the last brode was Labas and the first Iacobs.
43 Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙe mai arziki, ya kasance mai manya-manyan garkuna, da bayi mata da maza, da raƙuma da kuma jakuna.
And the man became excedynge ryche and had many shepe maydeseruauntes menseruauntes camels and asses.

< Farawa 30 >