< Farawa 28 >

1 Saboda haka Ishaku ya kira Yaƙub, ya kuma albarkace shi, sa’an nan ya umarce shi ya ce, “Kada ka auri mace daga Kan’ana.
Isaac called Jacob, blessed him, and commanded him, "You must not take a wife from the daughters of Canaan.
2 Tashi nan da nan ka tafi Faddan Aram, zuwa gidan mahaifin mahaifiyarka Betuwel. Ka ɗauko wa kanka mata a can daga cikin’ya’ya matan Laban ɗan’uwan mahaifiyarka.
Arise, go to Paddan Aram, to the house of Bethuel your mother's father. Take a wife from there from the daughters of Laban, your mother's brother.
3 Bari Allah Maɗaukaki yă albarkace ka, yă kuma sa ka yi ta haihuwa ka riɓaɓɓanya har ka zama ƙungiyar jama’o’i.
May El Shaddai bless you, and make you fruitful, and multiply you, that you may be a company of peoples,
4 Bari Allah yă ba ka da kuma zuriyarka albarkar da ya ba wa Ibrahim, don ka amshi ƙasar da kake baƙunci, ƙasar da Allah ya ba wa Ibrahim.”
and give you the blessing of Abraham, to you, and to your descendants with you, that you may inherit the land where you travel, which God gave to Abraham."
5 Sa’an nan Ishaku ya sallami Yaƙub, ya kuwa tafi Faddan Aram, zuwa wurin Laban ɗan Betuwel mutumin Aram. Laban ne ɗan’uwan Rebeka, wadda take mahaifiyar Yaƙub da Isuwa.
Isaac sent Jacob away. He went to Paddan Aram to Laban, son of Bethuel the Aramean, Rebekah's brother, Jacob's and Esau's mother.
6 Yanzu Isuwa ya san cewa Ishaku ya albarkaci Yaƙub ya kuma aike shi zuwa Faddan Aram don yă auri mata daga can, ya kuma san cewa sa’ad da ya albarkace shi, ya umarce shi cewa, “Kada ka auro wata mace daga cikin Kan’aniyawa,”
Now Esau saw that Isaac had blessed Jacob and sent him away to Paddan Aram, to take him a wife from there, and that as he blessed him he gave him a command, saying, "You must not take a wife from the daughters of Canaan,"
7 ya kuma san cewa Yaƙub ya yi biyayya da mahaifinsa da kuma mahaifiyarsa, ya kuwa tafi Faddan Aram.
and that Jacob obeyed his father and his mother, and left for Paddan Aram.
8 Sai Isuwa ya gane cewa matan Kan’aniyawa ba su gamshi mahaifinsa Ishaku ba;
Esau saw that the daughters of Canaan did not please Isaac, his father.
9 saboda haka sai ya tafi wurin Ishmayel ya auri Mahalat,’yar’uwar Nebayiwot da kuma’yar Ishmayel ɗan Ibrahim, ban da matan da yake da su.
Esau went to Ishmael, and took, besides the wives that he had, Mahalath the daughter of Ishmael, Abraham's son, the sister of Nebaioth, to be his wife.
10 Yaƙub ya bar Beyersheba ya kama hanyar Haran.
Jacob went out from Beersheba, and went toward Haran.
11 Sa’ad da ya kai wani wuri, sai ya dakata domin yă kwana, gama rana ta riga ta fāɗi. Ya ɗauki dutse daga cikin duwatsun wurin, ya sa shi ya zama matashin kansa, sa’an nan ya kwanta don yă yi barci.
He came to a certain place, and stayed there all night, because the sun had set. He took one of the stones of the place, and put it under his head, and lay down in that place to sleep.
12 Ya yi mafarki inda ya ga wata matakalar hawa, tsaye a ƙasa, kanta ta kai sama, mala’ikun Allah kuwa suna hawa, suna sauka a kanta.
And he dreamed. And look, a stairway was set upon the earth, and its top reached to heaven. And look, the angels of God were ascending and descending on it.
13 A can bisantaUbangiji ya tsaya, ya kuma ce, “Ni ne Ubangiji Allah na mahaifinka Ibrahim da kuma Allah na Ishaku. Zan ba ka, kai da kuma zuriyarka, ƙasar da kake kwance a kai.
And God stood above it, and said, "I am the God of Abraham your grandfather, and the God of Isaac. The land on which you are lying I will give to you and to your descendants.
14 Zuriyarka za tă zama kamar ƙurar ƙasa, za ka kuma bazu zuwa yamma da kuma gabas, zuwa arewa da kuma kudu. Dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka da kuma ta wurin’ya’yanka.
Your descendants will be as the dust of the earth, and you will spread out to the west, and to the east, and to the north, and to the south. And through you and through your descendants will all the families of the earth be blessed.
15 Ina tare da kai, zan lura da kai duk inda ka tafi, zan kuma dawo da kai zuwa wannan ƙasa. Ba zan rabu da kai ba sai na cika abin da na yi maka alkawari.”
And look, I am with you, and will watch over you wherever you go, and will bring you again into this land. For I will not leave you, until I have done that which I have spoken of to you."
16 Sa’ad da Yaƙub ya farka daga barci, sai ya yi tunani ya ce, “Tabbatacce Ubangiji yana a wannan wuri, ban kuwa sani ba.”
Then Jacob woke up from his sleep, and said, "Surely God is in this place, and I did not know it."
17 Ya ji tsoro, ya kuma ce, “Wane irin wuri ne mai banrazana haka! Lalle wannan gidan Allah ne, kuma nan ne ƙofar sama.”
He was afraid, and said, "How awesome is this place. This is none other than God's house, and this is the gate of heaven."
18 Kashegari da sassafe, sai Yaƙub ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al’amudi, ya kuma zuba mai a kansa.
And Jacob rose up early in the morning, and took the stone that he had put under his head, and set it up as a standing-stone, and poured oil on top of it.
19 Ya kira wannan wuri Betel ko da yake dā ana kiran birnin Luz ne.
He called the name of that place Bethel, though previously the city was named Luz.
20 Sa’an nan Yaƙub ya yi alkawari cewa, “In Allah zai kasance tare da ni yă kuma lura da ni a wannan tafiya, yă kuma ba ni abinci in ci da tufafi in sa,
Then Jacob made a vow, saying, "If God will be with me, and will watch over me on this journey I am taking, and will give me food to eat, and clothing to put on,
21 har in dawo lafiya zuwa gidan mahaifina, to, Ubangiji zai zama Allahna
so that I return to my father's house safely, then he will be my God,
22 kuma wannan dutsen da na kafa al’amudi, zai zama gidan Allah, kuma dukan abin da ka ba ni zan ba ka kashi ɗaya bisa goma.”
and this stone, which I have set up as a standing-stone, will be God's house. Of all that you will give me I will surely give the tenth to you."

< Farawa 28 >