< Farawa 27 >

1 Sa’ad da Ishaku ya tsufa idanunsa suka raunana har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa ya ce masa, “Ɗana.” Isuwa kuwa ya amsa, ya ce “Ga ni.”
It happened, that when Isaac was old, and his eyesight was failing so that he could not see, he called Esau his elder son, and said to him, "My son?" He said to him, "Here I am."
2 Ishaku ya ce, “Yanzu na tsufa kuma ban san ranar mutuwata ba.
He said, "Look, I am old now. I do not know the day of my death.
3 Saboda haka yanzu, ka ɗauki makamanka, kwari da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama.
Now therefore, please take your weapons, your quiver and your bow, and go out to the field, and hunt down a wild animal for me.
4 Ka shirya mini irin abinci mai daɗin da nake so, ka kawo mini in ci, domin in sa maka albarka kafin in mutu.”
Make me the tasty food that I love and bring it to me to eat, so that I may bless you before I die."
5 Ashe, Rebeka tana ji sa’ad da Ishaku ya yi wa ɗansa Isuwa magana. Da Isuwa ya tafi jeji don yă farauto nama yă kawo,
Rebekah heard when Isaac spoke to Esau his son. And Esau went out to the field to hunt for a wild animal and bring it back to his father.
6 sai Rebeka ta ce wa ɗanta Yaƙub, “Ka ji nan, na ji mahaifinka ya ce wa ɗan’uwanka Isuwa,
And Rebekah spoke to Jacob her son, saying, "Look, I heard your father speak to Esau your brother, saying,
7 ‘Kawo mini nama ka shirya mini abinci mai daɗi don in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in mutu.’
'Bring me a wild animal and prepare for me some tasty food, that I may eat it and bless you in my presence before my death.'
8 Saboda haka ɗana, ka saurara da kyau ka kuma yi abin da na faɗa maka.
Now therefore, my son, obey my voice according to that which I command you.
9 Je garke ka kawo mini awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi wa mahaifinka, kamar yadda dai yake so.
Go now to the flock, and get me from there two choice young goats. I will prepare them in a tasty way for your father, the way he likes it.
10 Sa’an nan ka kai wa mahaifinka yă ci, domin yă sa maka albarka kafin yă mutu.”
You shall bring it to your father, that he may eat, so that he may bless you before his death."
11 Yaƙub ya ce wa mahaifiyarsa Rebeka, “Amma ɗan’uwana Isuwa mutum ne mai gashi a jiki, ni kuma jikina sumul yake.
Jacob said to Rebekah his mother, "Look, Esau my brother is a hairy man, and I am a smooth man.
12 A ce baba ya tattaɓa ni fa? Zai zama kamar ina ruɗunsa ne, wannan fa zai jawo mini la’ana a maimakon albarka.”
What if my father touches me? I will seem to him as a deceiver, and I would bring a curse on myself, and not a blessing."
13 Mahaifiyarsa ta ce masa, “Ɗana, bari la’anar tă fāɗo a kaina. Kai dai yi abin da na faɗa, jeka ka kawo mini su.”
His mother said to him, "Let your curse be on me, my son. Only obey my voice, and go get them for me."
14 Sai ya tafi ya kamo su, ya kawo wa mahaifiyarsa, ta kuwa shirya abinci mai daɗi, yadda mahaifinsa yake so.
He went, and got them, and brought them to his mother. His mother prepared some tasty food, just the way his father liked it.
15 Sa’an nan Rebeka ta ɗauki riguna mafi kyau na Isuwa babban ɗanta, waɗanda take da su a gida ta sa wa ƙaramin ɗanta Yaƙub.
Rebekah took the good clothes of Esau, her elder son, which were with her in the house, and put them on Jacob, her younger son.
16 Sai ta mamanne gashin awakin nan biyu a hannuwansa da bayan wuyarsa wanda ba gashi.
She put the skins of the young goats on his hands, and on the smooth of his neck.
17 Sa’an nan ta ba wa ɗanta Yaƙub abinci mai daɗi da kuma burodin da ta yi.
She handed the tasty food and the bread which she had prepared to her son Jacob.
18 Shi kuwa ya tafi wurin mahaifinsa ya ce, “Babana.” Shi kuma ya amsa “I, ɗana, wane ne?”
He came to his father, and said, "My father?" He said, "Here I am. Who are you, my son?"
19 Yaƙub ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini. Ina roƙonka tashi ka zauna ka ci naman, domin ka sa mini albarkarka.”
Jacob said to his father, "I am Esau your firstborn. I have done what you asked me to do. Please sit up and eat what I hunted so that you can bless me."
20 Ishaku ya tambayi ɗansa, “Yaya aka yi ka samo shi da sauri haka, ɗana?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Ubangiji Allahnka ne ya ba ni nasara.”
Isaac said to his son, "How is it that you have found it so quickly, my son?" He said, "Because your God gave me success."
21 Sai Ishaku ya ce wa Yaƙub, “Zo kusa don in taɓa ka, ɗana, domin in sani ko tabbatacce kai ne ɗana Isuwa ko babu.”
Isaac said to Jacob, "Please come near, that I may feel you, my son, whether you are really my son Esau or not."
22 Yaƙub kuwa ya matsa kusa da mahaifinsa Ishaku, wanda ya tattaɓa shi, sa’an nan ya ce, “Muryan nan dai, muryar Yaƙub ce, amma hannuwan, hannuwan Isuwa ne.”
Jacob went near to Isaac his father. He felt him, and said, "The voice is Jacob's voice, but the hands are the hands of Esau."
23 Bai gane shi ba, gama hannuwansa suna da gashi kamar na ɗan’uwansa Isuwa, saboda haka ya albarkace shi.
He did not recognize him, because his hands were hairy like those of his brother Esau. So he blessed him.
24 Ya tambaya, “Tabbatacce kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa ya ce “Ni ne.”
He said, "Are you really my son Esau?" He said, "I am."
25 Sa’an nan ya ce, “Ɗana, kawo mini naman da ka farauto in ci, domin in sa maka albarka.” Yaƙub ya kawo masa ya kuwa ci; ya kuma kawo masa ruwan inabi ya kuma sha.
He said, "Bring it near to me, and I will eat of what my son caught so that I can bless you." He brought it near to him, and he ate. He brought him wine, and he drank.
26 Sa’an nan mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Zo nan, ɗana ka sumbace ni.”
His father Isaac said to him, "Come near now, and kiss me, my son."
27 Saboda haka ya je gunsa ya sumbace shi. Sa’ad da Ishaku ya ji ƙanshin rigunansa, sai ya sa masa albarka ya ce, “Aha, ƙanshin ɗana yana kama da ƙanshin jejin da Ubangiji ya sa wa albarka ne.
He came near, and kissed him. He smelled the scent of his clothing, and blessed him, and said, "Look, the scent of my son is as the scent of a field which God has blessed.
28 Allah yă ba ka daga raɓar sama da kuma yalwar ƙasa, yalwar hatsi da sabon ruwan inabi.
God give you of the dew of the sky, of the fatness of the earth, and plenty of grain and new wine.
29 Bari al’ummai su bauta maka mutane kuma su rusuna maka. Ka zama shugaba a kan’yan’uwanka bari kuma’ya’yan mahaifiyarka su rusuna maka. Bari waɗanda suka la’anta ka, su la’antu; waɗanda kuma suka sa maka albarka, su sami albarka.”
Let peoples serve you, and nations bow down to you. Be lord over your brothers. Let your mother's sons bow down to you. Cursed be everyone who curses you. Blessed be everyone who blesses you."
30 Bayan Ishaku ya gama sa masa albarka, Yaƙub yana fita daga mahaifinsa ke nan, sai ga ɗan’uwansa Isuwa ya dawo daga farauta.
It happened, as soon as Isaac had finished blessing Jacob, and Jacob had just left the presence of Isaac his father, that Esau his brother came in from his hunting.
31 Shi ma ya shirya abinci mai daɗi ya kawo wa mahaifinsa. Sa’an nan ya ce masa, “Babana, tashi ka zauna ka ci daga abin da na farauto, domin ka sa mini albarka.”
He also made some tasty food, and brought it to his father. He said to his father, "Let my father get up and eat of what his son caught, so that you may bless me."
32 Mahaifinsa Ishaku ya tambaye shi, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.”
Isaac his father said to him, "Who are you?" He said, "I am your son, your firstborn, Esau."
33 Ishaku ya yi makyarkyata ƙwarai ya ce, “To, wane ne wannan da ya farauto nama ya kawo mini kafin ka zo, har na ci na kuma sa masa albarka? Tabbatacce zai zama mai albarka!”
Isaac trembled violently, and said, "Who was it then that hunted an animal and brought it to me, and I ate it all before you came, and have blessed him? Yes, he will be blessed."
34 Sa’ad da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya fashe da kuka mai zafi kuma da ƙarfi, ya ce wa mahaifinsa, “Ka albarkace ni, ni ma, baba!”
When Esau heard the words of his father, he cried out loudly and bitterly, and said to his father, "Bless me, even me also, my father."
35 Amma ya ce, “Ɗan’uwanka ya zo da makirci ya karɓi albarkarka.”
He said, "Your brother came with deceit, and has taken away your blessing."
36 Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yaƙub ba? Ya yi mini ƙwace sau biyu ke nan; ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi yanzu kuma ya karɓi albarkata.” Sa’an nan ya yi tambaya, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?”
He said, "Isn't he rightly named Jacob? For he has taken what should have been mine these two times. He took away my birthright. Look, now he has taken away my blessing." He said, "Haven't you reserved a blessing for me?"
37 Ishaku ya amsa wa Isuwa, “Na mai da shi shugaba a kanka, na sa dukan dangoginsa su zama bayinsa, na kuma ba shi hatsi da sabon ruwan inabi. Saboda haka me kuma zan yi maka ɗana?”
Isaac answered Esau, "Look, I have made him your lord, and I have made all of his brothers his servants. And I have sustained him with grain and new wine. What then can I do for you, my son?"
38 Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Ka albarkace ni ni ma, baba!” Sai Isuwa ya ɗaga murya ya yi kuka.
Esau said to his father, "Have you but one blessing, my father? Bless me, even me also, my father." Esau lifted up his voice, and wept.
39 Mahaifinsa Ishaku ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni’imar ƙasar za tă nisanci mazauninka. Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za tă nisance ka.
Isaac his father answered him, "Look, of the fatness of the earth will be your dwelling, and of the dew of the sky from above.
40 Za ka rayu ta wurin takobi za ka kuwa bauta wa ɗan’uwanka. Amma sa’ad da ka ɓalle, za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.”
By your sword will you live, and you will serve your brother. It will happen, when you will break loose, that you shall shake his yoke from off your neck."
41 Isuwa ya riƙe Yaƙub a zuciya saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Ya ce wa kansa, “Kwanakin mutuwar mahaifina sun yi kusa; sa’an nan zan kashe ɗan’uwana Yaƙub.”
Esau hated Jacob because of the blessing with which his father blessed him. Esau said in his heart, "The days of mourning for my father are at hand. Then I will kill my brother Jacob."
42 Sa’ad da aka faɗa wa Rebeka abin da babban ɗanta Isuwa ya faɗa, sai ta kira ɗanta Yaƙub ta ce masa, “Ɗan’uwanka Isuwa yana ta’azantar da kansa da tunanin kashe ka.
The words of Esau, her elder son, were told to Rebekah. She sent and called Jacob, her younger son, and said to him, "Look, your brother Esau comforts himself about you by planning to kill you.
43 To, fa, ɗana, yi abin da na ce; gudu nan take zuwa wurin ɗan’uwana Laban a Haran.
Now therefore, my son, obey my voice. Arise, flee to Laban, my brother, in Haran.
44 Zauna tare da shi na ɗan lokaci sai ɗan’uwanka ya huce.
Stay with him a few days, until your brother's fury turns away;
45 Sa’ad da ɗan’uwanka ya daina fushi da kai, ya kuma manta da abin da ka yi masa, zan aika don ka dawo daga can. Don me zan rasa ku biyu a rana guda?”
until your brother's anger against you subsides, and he forgets what you have done to him. Then I will send for you and get you from there. Why should I lose both of you in one day?"
46 Sa’an nan Rebeka ta ce wa Ishaku, “Ni fa na gaji da matan Hittiyawan nan. In Yaƙub ya auri mata daga cikin matan ƙasan nan, wato, daga matan Hittiyawa irin waɗannan, rayuwata ba za tă daɗa mini kome ba.”
Rebekah said to Isaac, "I loathe my life because of the daughters of Heth. If Jacob takes a wife from the daughters of Heth, like these, from the daughters of the land, what good is my life?"

< Farawa 27 >