< Farawa 23 >

1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
And the life of Sarrha was an hundred and twenty-seven years.
2 Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
And Sarrha died in the city of Arboc, which is in the valley, this is Chebron in the land of Chanaan; and Abraam came to lament for Sarrha and to mourn.
3 Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
And Abraam stood up from before his dead; and Abraam spoke to the sons of Chet, saying,
4 “Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
I am a sojourner and a stranger among you, give me therefore possession of a burying-place among you, and I will bury my dead away from me.
5 Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
And the sons of Chet answered to Abraam, saying, Not so, Sir,
6 “Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
but hear us; you are in the midst of us a king from God; bury your dead in our choice sepulchres, for not one of us will by any means withhold his sepulchre from you, so that you should not bury your dead there.
7 Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
And Abraam rose up and did obeisance to the people of the land, to the sons of Chet.
8 Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
And Abraam spoke to them, saying, If you have it in your mind that I should bury my dead out of my sight, listen to me, and speak for me to Ephron the son Saar.
9 domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
And let him give me the double cave which he has, which is in a part of his field, let him give it me for the money it is worth for possession of a burying-place among you.
10 Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
Now Ephron was sitting in the midst of the children of Chet, and Ephron the Chettite answered Abraam and spoke in the hearing of the sons of Chet, and of all who entered the city, saying,
11 Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
Attend to me, my lord, and hear me, I give to you the field and the cave which is in it; I have given it you before all my country men; bury your dead.
12 Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
And Abraam did obeisance before the people of the land.
13 ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
And he said in the ears of Ephron before the people of the land, Since you are on my side, hear me; take the price of the field from me, and I will bury my dead there.
14 Efron ya ce wa Ibrahim,
But Ephron answered Abraam, saying,
15 “Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
Nay, my lord, I have heard indeed, the land [is worth] four hundred silver didrachmas, but what can this be between me and you? nay, do you bury your dead.
16 Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
And Abraam listened to Ephron, and Abraam rendered to Ephron the money, which he mentioned in the ears of the sons of Chet, four hundred didrachmas of silver approved with merchants.
17 Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
And the field of Ephron, which was in Double Cave, which is opposite Mambre, the field and the cave, which was in it, and every tree which was in the field, and whatever is in its borders round about, were made sure in its borders round about, were made sure
18 ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
to Abraam for a possession, before the sons of Chet, and all that entered into the city.
19 Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
After this Abraam buried Sarrha his wife in the Double Cave of the field, which is opposite Mambre, this is Chebron in the land of Chanaan.
20 Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.
So the field and the cave which was in it were made sure to Abraam for possession of a burying place, by the sons of Chet.

< Farawa 23 >