< Farawa 22 >

1 Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
It happened after these things, that God tested Abraham, and said to him, "Abraham, Abraham." He said, "Here I am."
2 Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
He said, "Now take your son, your only one, whom you love, even Isaac, and go into the land of Moriah. Offer him there as a burnt offering on one of the mountains which I will tell you of."
3 Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
Abraham rose early in the morning, and saddled his donkey, and took two of his young men with him, and Isaac his son. He split the wood for the burnt offering, and rose up, and went to the place of which God had told him.
4 A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
On the third day Abraham lifted up his eyes, and saw the place far off.
5 Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
Abraham said to his young men, "Stay here with the donkey. The boy and I will go over there, and we will worship, and come back to you."
6 Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
Abraham took the wood of the burnt offering and laid it on Isaac his son. He took in his hand the fire and the knife. They both went together.
7 sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
Isaac spoke to Abraham his father, and said, "My father?" He said, "Here I am, my son." He said, "Here is the fire and the wood, but where is the lamb for a burnt offering?"
8 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
Abraham said, "God will provide himself the lamb for a burnt offering, my son." So they both went together.
9 Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
They came to the place which God had told him of. Abraham built the altar there and arranged the wood, and bound his son Isaac and placed him on the altar, on top of the wood.
10 Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
Abraham reached out his hand, and took the knife to kill his son.
11 Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
But an angel of God called to him out of the sky, and said, "Abraham, Abraham." And he said, "Here I am."
12 Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
He said, "Do not lay your hand on the boy, neither do anything to him. For now I know that you fear God, seeing you have not withheld your son, your only one, from me."
13 Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
And Abraham looked up and saw behind him a ram caught in the thicket by his horns. And Abraham went and took the ram, and offered him up as a burnt offering instead of his son.
14 Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
Abraham called the name of that place Elohim Yireh. As it is said to this day, "On the mountain, God will provide."
15 Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
The angel of God called to Abraham a second time out of the sky,
16 ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
and said, "I have sworn by myself," says YHWH, "because you have done this thing, and have not withheld your son, your only one, from me,
17 tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
I will indeed bless you, and I will greatly multiply your offspring like the stars of the sky, and like the sand which is on the seashore; and your offspring will possess the gate of their enemies.
18 ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
And through your offspring all the nations of the earth will be blessed, because you have obeyed my voice."
19 Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
So Abraham returned to his young men, and they rose up and went together to Beersheba. Abraham lived at Beersheba.
20 Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
It happened after these things, that it was told Abraham, saying, "Look, Milcah also has borne children to your brother Nahor:
21 ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
Uz his firstborn, Buz his brother, Kemuel the father of Aram,
22 Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
Kesed, Hazo, Pildash, Jidlaph, and Bethuel."
23 Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
Bethuel became the father of Rebekah. These eight Milcah bore to Nahor, Abraham's brother.
24 Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.
His secondary wife, whose name was Reumah, also bore Tebah, Gaham, Tahash, and Maacah.

< Farawa 22 >