< Farawa 19 >

1 Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Un tie divi eņģeļi vakarā nonāca Sodomā, un Lats sēdēja Sodomas vārtos. Un tos ieraudzījis Lats cēlās un gāja tiem pretī un nometās uz savu vaigu pie zemes
2 Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
Un sacīja: redzi, mani kungi, ņemiet lūdzami mājas vietu pie sava kalpa un palieciet šo nakti un mazgājiet savas kājas; tad rītā cēlušies varat iet savu ceļu. Un tie sacīja: nē, bet mēs gribam palikt pa nakti uz ielas.
3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
Bet viņš tos lūgdams lūdza, lai tie pie viņa mājotu; un tie iegāja viņa namā, un viņš tiem taisīja mielastu, cepdams neraudzētas karašas, un tie ēda.
4 Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
Pirms ne kā tie apgūlās, Sodomas pilsētas ļaudis apstāja to namu, jauni un veci, viss tas pulks no visām malām,
5 Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
Un aicināja Latu un sacīja uz to: kur tie vīri, kas šo nakti pie tevis nākuši? Izved tos pie mums ārā, ka tos atzīstam.
6 Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
Tad Lats izgāja pie tiem ārā priekš durvīm, un aizslēdza durvis aiz sevis un sacīja:
7 ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
Brāļi, nedariet jel tādu grēku.
8 Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
Redziet, man ir divas meitas, kas nav atzinušas vīra, tās izvedīšu pie jums, un dariet ar tām, kā patīk, - tikai šiem vīriem nedariet nekā, jo tāpēc tie nākuši mana jumta pavēnī.
9 Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
Tad tie sacīja: atkāpies nost! Un tie sacīja: šis viens ir atnācis kā svešinieks un grib valdīt? Nu tev vairāk ļauna darīsim nekā viņiem.
10 Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
Un mākdamies tie mācās virsū tam vīram, Latam, un nāca durvis uzlauzt. Bet tie vīri izstiepa ārā savu roku un ierāva Latu pie sevis namā un aizslēdza durvis,
11 Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
Un apstulboja tos ļaudis priekš nama durvīm, mazos un lielos, tā ka tie piekusa pēc durvīm grābstīdamies.
12 Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
Tad tie vīri sacīja uz Latu: vai tev še vēl kāds znots vai dēli vai meitas vai cits kāds, kas tev pieder šai pilsētā, - izved tos no šās vietas.
13 gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
Jo mēs samaitāsim šo vietu, tāpēc ka tā brēkšana par viņu ir liela Tā Kunga priekšā, un Tas Kungs mūs ir sūtījis to samaitāt.
14 Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
Un Lats izgāja un runāja uz saviem znotiem, kas viņa meitas gribēja apņemt, un sacīja: ceļaties un ejat ārā no šās vietas, jo Tas Kungs samaitās šo pilsētu. Bet tiem znotiem viņš izlikās tā kā smieklus runājot.
15 Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
Un kad gaisma ausa, tad tie eņģeļi Latu skubināja sacīdami: celies, ņem savu sievu un savas divas meitas, kas tev ir, ka tu neietu bojā šīs pilsētas noziegumā.
16 Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
Bet viņš kavējās; un tie vīri satvēra viņa roku un viņa sievas roku un viņa divēju meitu roku, tāpēc ka Tas Kungs viņu žēloja, un tie to izveda un to palaida ārpus pilsētas.
17 Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
Un kad tie tos bija izveduši ārā, tad viņš sacīja: Izglāb jel savu dzīvību, neskaties atpakaļ un nestāvi nekur šinī klajumā; glābies kalnā, ka neej bojā.
18 Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
Un Lats sacīja uz tiem: ak nē, Kungs!
19 Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
Redzi jel, tavs kalps ir atradis žēlastību tavās acīs, un varen liela ir tava žēlošana, ko tu man esi darījis, izglābdams manu dzīvību; bet es nespēju glābties kalna galā, lai man ļaunums neuznāk un es nemirstu.
20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
Redzi jel, šī pilsēta ir tuvu klāt, uz turieni bēgt, un tā ir maza; tur es gribu glābties, - vai tā nav maza? - Ka es palieku dzīvs.
21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
Un viņš uz to sacīja: redzi, arī šinī lietā es tevi esmu uzlūkojis, ka es nesamaitāšu to pilsētu, par ko tu esi runājis.
22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
Steidzies, glābies turp, jo es nekā nevaru darīt, tiekams tu uz turieni neesi nonācis. Tādēļ tās pilsētas vārdu sauc Coāru (t.i. maza).
23 A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
Saule uzlēca pār zemi, kad Lats nonāca Coārā.
24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
Un Tas Kungs lika līt sēram un ugunij uz Sodomu un Gomoru no Tā Kunga, no debesīm.
25 Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
Un viņš izpostīja tās pilsētas un visu to apgabalu un visus to pilsētu iedzīvotājus, ir zemes augļus.
26 Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
Un viņa sieva skatījās atpakaļ un palika par sālsstabu.
27 Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
Un Ābraams cēlās it agri uz to vietu, kur viņš bija stāvējis priekš Tā Kunga vaiga,
28 Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
Un skatījās uz Sodomas un Gomoras pusi un uz visu to apgabalu, un redzi, dūmi cēlās no zemes, tā kā kāda cepļa dūmi.
29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
Un notikās, kad Dievs šī apgabala pilsētas samaitāja, tad viņš pieminēja Ābrahāmu un izveda Latu no tā posta, kad viņš tās pilsētas izpostīja, kur Lats mita.
30 Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
Un Lats gāja no Coāras uz augšu un mita kalnos, un viņa divas meitas līdz ar viņu; jo viņam bija bail Coārā mist; un viņš dzīvoja kādā alā līdz ar savām abām meitām.
31 Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
Un tā pirmdzimušā sacīja uz to jaunāko: mūsu tēvs ir vecs, un vīra nav virs zemes, kas pie mums nāktu pēc visas pasaules ieraduma.
32 Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
Nāc, dosim savam tēvam vīnu dzert un gulēsim pie tā un paturēsim dzīvu dzimumu no sava tēva.
33 A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
Un tās deva savam tēvam vīnu dzert tanī naktī, un tā pirmdzimušā nāca un gulēja pie sava tēva, un viņš to nenomanīja, kad tā apgūlās, nedz kad tā cēlās.
34 Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
Un no rīta tā pirmdzimušā sacīja uz to jaunāko: redzi, izgājušo nakti es esmu gulējusi pie sava tēva; dosim viņam arī šo nakti vīnu dzert, tad ieej tu un guli pie tā, ka dzimumu gādājam no sava tēva.
35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
Un tās arī tanī naktī deva savam tēvam vīnu dzert, un tā jaunākā cēlās un gulēja pie tā, un tas nenomanīja, kad tā apgūlās, nedz kad tā cēlās.
36 Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
Un Lata abas meitas tapa grūtas no sava tēva.
37 ’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
Un tā pirmdzimušā dzemdēja dēlu un nosauca viņa vārdu Moabs, šis ir Moabiešu tēvs līdz šai dienai.
38 ’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.
Un tā jaunākā dzemdēja arī dēlu un nosauca viņa vārdu Ben-Ammi: šis ir Amona bērnu tēvs līdz šai dienai.

< Farawa 19 >