< Farawa 17 >

1 Sa’ad da Abram ya yi shekaru 99, sai Ubangiji ya bayyana a gare shi ya ce, ni “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi tafiya a gabana ka kuma zama marar abin zargi.
A kad Avramu bi devedeset i devet godina, javi mu se Gospod i reèe mu: ja sam Bog svemoguæi, po mojoj volji živi i budi pošten.
2 Zan tabbatar da alkawarina tsakanina da kai, zan kuma ƙara zuriyarka ta yi yawa.”
I uèiniæu zavjet izmeðu sebe i tebe, i vrlo æu te umnožiti.
3 Abram ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, Allah kuma ya ce masa,
A Avram pade nièice. I Gospod mu još govori i reèe:
4 “Gare ni kam, wannan shi ne alkawarina da kai, za ka zama mahaifin al’ummai masu yawa.
Od mene evo zavjet moj s tobom da æeš biti otac mnogim narodima.
5 Ba za a ƙara kiranka Abram ba; sunanka zai zama Ibrahim, gama na mai da kai uban al’ummai masu yawa.
Zato se više neæeš zvati Avram, nego æe ti ime biti Avraam, jer sam te uèinio ocem mnogih naroda;
6 Zan sa ka azurta sosai, zan yi al’ummai daga cikinka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka,
Daæu ti porodicu vrlo veliku, i naèiniæu od tebe narode mnoge, i carevi æe izaæi od tebe.
7 zan kafa alkawarina kamar madawwamin alkawari tsakanina da kai da kuma zuriyarka bayanka har tsararraki masu zuwa, in zama Allahnka da kuma Allahn zuriyarka a bayanka.
A postavljam zavjet svoj izmeðu sebe i tebe i sjemena tvojega nakon tebe od koljena do koljena, da je zavjet vjeèan, da sam Bog tebi i sjemenu tvojemu nakon tebe;
8 Dukan ƙasar Kan’ana inda kake baƙo a yanzu, zan ba da ita a matsayin madawwamiyar mallaka gare ka da kuma zuriyarka a bayanka, zan kuma zama Allahnsu.”
I daæu tebi i sjemenu tvojemu nakon tebe zemlju u kojoj si došljak, svu zemlju Hanansku u državu vjeènu, i biæu im Bog.
9 Sa’an nan Allah ya ce wa Ibrahim. “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, kai da zuriyarka bayanka, har tsararraki masu zuwa.
I reèe Bog Avramu: ti pak drži zavjet moj, ti i sjeme tvoje nakon tebe od koljena do koljena.
10 Wannan shi ne alkawarina da kai da kuma zuriyarka a bayanka, alkawarin da za ka kiyaye ke nan. Kowane namiji a cikinku kuwa za a yi masa kaciya.
A ovo je zavjet moj izmeðu mene i vas i sjemena tvojega nakon tebe, koji æete držati: da se obrezuje izmeðu vas sve muškinje.
11 Za ku yi kaciya, za tă kuma zama alamar alkawari tsakanina da kai.
A obrezivaæete okrajak tijela svojega, da bude znak zavjeta izmeðu mene i vas.
12 Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan zamananku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba.
Svako muško dijete kad mu bude osam dana da se obrezuje od koljena do koljena, rodilo se u kuæi ili bilo kupljeno za novce od kojih god stranaca, koje ne bude od sjemena tvojega.
13 Ko haifaffe a gidanka ko an sayo da kuɗi, dole a yi musu kaciya. Alkawarina cikin jikinku zai kasance madawwamin alkawari.
Da se obrezuje koje se rodi u kuæi tvojoj i koje se kupi za novce tvoje; tako æe biti zavjet moj na tijelu vašem zavjet vjeèan.
14 Kowane namijin da ba a yi masa kaciya a jiki ba, za a fid da shi daga cikin mutanensa; domin ya karya alkawarina.”
A neobrezano muško, kojemu se ne obreže okrajak tijela njegova, da se istrijebi iz naroda svojega, jer pokvari zavjet moj.
15 Allah ya kuma ce wa Ibrahim, “Game da Saira matarka kuwa, ba za ka ƙara kiranta Saira ba, sunanta zai zama Saratu.
I još reèe Bog Avramu: a Saru ženu svoju ne zovi je više Sara nego neka joj bude ime Sara.
16 Zan sa mata albarka, ban da haka ma, zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za tă kuwa zama mahaifiyar al’ummai; sarakunan mutane za su fito daga gare ta.”
I ja æu je blagosloviti, i daæu ti sina od nje; blagosloviæu je, i biæe mati mnogim narodima, i carevi narodima izaæi æe od nje.
17 Ibrahim ya rusuna da fuskarsa har ƙasa, ya yi dariya, ya ce wa kansa, “Za a haifi ɗa wa mutum mai shekaru ɗari? Saratu za tă haifi ɗa tana da shekaru tasa’in?”
Tada pade Avram nièice, i nasmija se govoreæi u srcu svojem: eda æe se èovjeku od sto godina roditi sin? i Sari? eda æe žena od devedeset godina roditi?
18 Ibrahim ya kuma ce wa Allah, “Me zai hana a dai bar Ishmayel kawai yă gāji alkawarin nan da ka yi mini.”
I Avram reèe Bogu: neka živ bude Ismailo pred tobom!
19 Sai Allah ya ce, “Duk da haka dai, matarka Saratu za tă haifi maka ɗa; za ka kuma kira shi Ishaku. A kansa zan tabbatar da madawwamin alkawarina, da kuma ga zuriyarsa da za su zo bayansa.
I reèe Bog: zaista Sara žena tvoja rodiæe ti sina, i nadjeæeš mu ime Isak; i postaviæu zavjet svoj s njim da bude zavjet vjeèan sjemenu njegovu nakon njega.
20 Game da Ishmayel kuwa, na ji ka. Tabbatacce zan albarkace shi, zan sa yă azurta, zai kuma ƙaru ƙwarai. Zai zama mahaifin masu mulki goma sha biyu, zan kuma maishe shi babban al’umma!
A i za Ismaila uslišio sam te; evo blagoslovio sam ga, i daæu mu porodicu veliku, i umnožiæu ga veoma; i rodiæe dvanaest knezova, i uèiniæu od njega velik narod.
21 Amma dai zan kafa alkawarina da Ishaku wanda Saratu za tă haifa maka war haka shekara mai zuwa.”
A zavjet svoj uèiniæu s Isakom kad ti ga rodi Sara, do godine u ovo doba.
22 Da ya gama magana da Ibrahim, sai Allah ya tashi daga gare shi.
I Bog izgovorivši otide od Avrama gore.
23 A wannan rana, Ibrahim ya ɗauki ɗansa Ishmayel da dukan waɗanda aka haifa cikin gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji a cikin gidansa kaciya kamar yadda Allah ya faɗa masa.
I Avram uze Ismaila sina svojega i sve koji se rodiše u domu njegovu i koje god bješe kupio za svoje novce, sve muškinje od domaæih svojih; i obreza okrajak tijela njihova u isti dan, kao što mu kaza Bog.
24 Ibrahim yana da shekara tasa’in da tara sa’ad da aka yi masa kaciya,
A bješe Avramu devedeset i devet godina kad obreza okrajak tijela svojega.
25 Ishmayel ɗansa kuma yana da shekara goma sha uku.
A Ismailu sinu njegovu bješe trinaest godina kad mu se obreza okrajak tijela njegova.
26 Aka yi wa Ibrahim da ɗansa Ishmayel kaciya a rana ɗaya.
U jedan dan obreza se Avram i sin mu Ismailo,
27 Aka yi wa kowane namiji a gidan Ibrahim kaciya, da waɗanda aka haifa a gidansa, da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙo.
I svi domašnji njegovi, roðeni u kuæi i kupljeni za novce od stranaca, biše obrezani s njim.

< Farawa 17 >