< Farawa 14 >

1 A zamanin Amrafel sarkin Shinar, shi da Ariyok sarkin Ellasar, Kedorlayomer sarkin Elam, da kuma Tidal sarkin Goyim
And it came to pass, in the days of Amraphel, king of Shinar, Arioch, king of Ellasar, —Chedorlaomer king of Elam, and Tidal king of Goim,
2 suka tafi don su yaƙi Bera sarkin Sodom, Birsha sarkin Gomorra, Shinab sarkin Adma, Shemeber sarkin Zeboyim, da kuma sarkin Bela (wato, Zowar).
that they made war, with Bera, king of Sodom, and with Birsha, king of Gomorrah, —Shinab, king of Admah, and Shemeber, king of Zeboim, and the king of Bela—the same, is Zoar.
3 Dukan waɗannan sarakuna na bayan nan suka haɗa kai a Kwarin Siddim (Teku Gishiri).
All these, joined together in the valley of the open fields, the same, is the Salt Sea.
4 Shekara goma sha biyu suna bauta wa Kedorlayomer, amma a shekara ta sha uku sai suka yi tawaye.
Twelve years, had they served Chedorlaomer, —but in the thirteenth year had they rebelled;
5 A shekara ta goma sha huɗu, Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi suka tafi suka cinye Refahiyawa a Ashterot Karnayim, Zuziyawa a Ham, Emawa a Shabe Kiriyatayim,
and in the fourteenth year, had Chedorlaomer come in and the kings who were with him, so they smote the Rephaim in Ashteroth-karnaim, and the Zuzim in Ham, —and the Emim, in Shaveh-kiriathaim;
6 da Horiyawa a ƙasar tudun Seyir har zuwa El Faran kusa da hamada.
and the Horites in their Mount Seir, —as far as El-paran, which is by the desert.
7 Sa’an nan suka juya suka tafi En Mishfat (wato, Kadesh), suka cinye dukan ƙasar Amalekawa, da kuma Amoriyawa waɗanda suke zaune a Hazazon Tamar.
So they returned and came in unto En-mishpat, the same, is Kadish, and smote all the field of the Amalekites, —and the Amorites also that dwelt in Hazazon-tamar,
8 Sai sarkin Sodom, sarkin Gomorra, sarkin Adma, sarkin Zeboyim da sarkin Bela (wato, Zowar), suka fita suka ja dāgā a Kwarin Siddim
Thus then went forth the King of Sodom and the king of Gomorrah, and the king of Admah and the king of Zeboim, and the king of Bela the same, is Zoar—and set themselves in array against them for battle, in the valley of the open fields:
9 gāba da Kedorlayomer sarkin Elam, Tidal sarkin Goyim, Amrafel sarkin Shinar da Ariyok sarkin Ellasar; sarakuna huɗu gāba da biyar.
against Chedorlaomer king of Elam, and Tidal king of Goim, and Amraphel king of Shinar, and Arioch king of Ellasar, —four kings against five.
10 Kwarin Siddim kuwa ya cika da ramummukan kwalta, sa’ad da sarakunan Sodom da Gomorra suka gudu kuwa, waɗansu mutane suka fāɗa cikin ramummukan kwaltan, sauran kuwa suka gudu zuwa tuddai.
Now, the valley of the open fields, had many pits of bitumen, so the king of Sodom and Gomorrah fled, and fell there, —while, they who remained, towards a mountain, fled.
11 Sarakunan nan huɗu suka washe dukan kayayyakin Sodom da Gomorra, da kuma dukan abincinsu, sa’an nan suka tafi.
And they took all the goods of Sodom and Gomorrah and all their food and went their way.
12 Suka kuma kama Lot ɗan ɗan’uwan Abram, wanda yake zaune a Sodom, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu.
And they took Lot, Abram’s brother’s son with his goods, and went their way, —he, being a dweller in Sodom.
13 Sai wani wanda ya tsira, ya zo ya faɗa wa Abram mutumin Ibraniyawa. Abram kuwa yana zama kusa da manyan itatuwan Mamre, Mamre mutumin Amoriyawa ne ɗan’uwan Eshkol da Aner, su kuwa abokan Abram ne.
Then came in a fugitive, and told Abram the Hebrew, —he, having his dwelling among the oaks of Mamre the Amorite brother of Eshcol and brother of Aner, they, also having a covenant with Abram.
14 Da Abram ya ji cewa an kama danginsa, sai ya tara horarrun mutane 318, da aka haifa a gidansa, ya bi sawun sarakunan da suka tafi da Lot, har Dan.
So Abram, hearing that his brother had been taken captive, drew forth his trained men born in his house three hundred and eighteen, and pursued as far as Dan.
15 Da dad dare, Abram ya rarraba mutanensa don su fāɗa wa sarakunan nan, ya ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewa da Damaskus.
And he divided himself against them by night, he, and his servants, and smote them, —and pursued them as far as Hobah, which was on the left of Damascus.
16 Ya washe su da kuma dukan kayayyakinsu, ya kuma dawo da Lot danginsa da mallakarsa, tare da mata da sauran mutane.
So he brought back all the goods, —yea Lot also his brother with his goods, did he bring back, and the women also, and the people.
17 Bayan Abram ya dawo daga cin Kedorlayomer da sarakunan da suka haɗa kai da shi a yaƙi, sai sarkin Sodom ya fito don yă tarye Abram a Kwarin Shabe (wato, Kwarin Sarki).
Then came forth the king of Sodom to meet him, after his return from the smiting of Chedorlaomer, and the kings who were with him, —into the vale of Shaveh the same, was the vale of the king.
18 Sai Melkizedek sarkin Salem ya kawo burodi da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Mafi Ɗaukaka,
Now Melchizedek king of Salem, had brought forth bread and wine, —he, being priest of GOD Most High.
19 ya albarkaci Abram yana cewa, “Allah Mafi Ɗaukaka Mahaliccin sama da ƙasa yă albarkace Abram.
So he blessed him and said, —Blessed be Abram of GOD Most High, possessor of [the] heavens and earth;
20 Kuma albarka ta tabbata ga Allah Mafi Ɗaukaka wanda ya ba da maƙiyanka a hannunka.” Sa’an nan Abram ya ba shi kashi ɗaya bisa goma na kome.
And blessed be GOD Most High, who hath delivered thine enemies into thy hand. So he gave unto him a tenth of all.
21 Sarkin Sodom ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanena da ka ƙwace daga hannun sarakunan nan kawai, ka riƙe kayayyakin don kanka.”
Then said the king of Sodom unto Abram, —Give unto me the persons, but the goods, take thou for thyself.
22 Amma Abram ya ce, wa sarkin Sodom, “Na ɗaga hannu ga Ubangiji Allah Mafi Ɗaukaka, Mahaliccin sama da ƙasa, na riga na rantse
And Abram said unto the king of Sodom, —I have lifted up my hand unto Yahweh GOD Most High, possessor of [the] heavens and earth:
23 cewa ba zan karɓi kome da yake naka ba, ko zare ko maɗaurin takalma, don kada ka ce, ‘Na azurta Abram.’
That not from a thread even unto a sandal-thong, —will I take, anything, that is thine, —Lest thou shouldst say, I, enriched Abram!
24 Ba zan karɓi kome ba, sai dai abin da mutanena suka ci da kuma rabon mutanen da suka tafi tare da ni, ga Aner, Eshkol, da Mamre. Bari su ɗauki rabonsu.”
Save only what the young men have eaten, and the share of the men who went with me, Aner, Eshcol, and Mamre, they may take their share.

< Farawa 14 >