< Farawa 10 >

1 Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
Now these are the generations of the sons of Noah, Shem Ham and Japheth: and unto them were sons born after the flood.
2 ’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
The sons of Japheth; Gomer, and Magog, and Madai, and Javan, and Tubal, and Meshech, and Tiras.
3 ’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
And the sons of Gomer; Ashkenaz, and Riphath, and Togarmah.
4 ’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
And the sons of Javan; Elishah, and Tarshish, Kittim, and Dodanim.
5 (Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
Of these were the isles of the nations divided in their lands, every one after his tongue; after their families, in their nations.
6 ’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
And the sons of Ham; Cush, and Mizraim, and Put, and Canaan.
7 ’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
And the sons of Cush; Seba, and Havilah, and Sabtah, and Raamah, and Sabteca: and the sons of Raamah; Sheba, and Dedan.
8 Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
And Cush begat Nimrod: he began to be a mighty one in the earth.
9 Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
He was a mighty hunter before the LORD: wherefore it is said, Like Nimrod a mighty hunter before the LORD.
10 Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
And the beginning of his kingdom was Babel, and Erech, and Accad, and Calneh, in the land of Shinar.
11 Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
Out of that land he went forth into Assyria, and builded Nineveh, and Rehoboth-Ir, and Calah,
12 da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
and Resen between Nineveh and Calah (the same is the great city).
13 Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
And Mizraim begat Ludim, and Anamim, and Lehabim, and Naphtuhim,
14 Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
and Pathrusim, and Casluhim (whence went forth the Philistines), and Caphtorim.
15 Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
And Canaan begat Zidon his firstborn, and Heth;
16 Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
and the Jebusite, and the Amorite, and the Girgashite;
17 Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
and the Hivite, and the Arkite, and the Sinite;
18 Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
and the Arvadite, and the Zemarite, and the Hamathite: and afterward were the families of the Canaanite spread abroad.
19 har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
And the border of the Canaanite was from Zidon, as thou goest toward Gerar, unto Gaza; as thou goest toward Sodom and Gomorrah and Admah and Zeboiim, unto Lasha.
20 Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
These are the sons of Ham, after their families, after their tongues, in their lands, in their nations.
21 Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
And unto Shem, the father of all the children of Eber, the elder brother of Japheth, to him also were children born.
22 ’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
The sons of Shem; Elam, and Asshur, and Arpachshad, and Lud, and Aram.
23 ’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
And the sons of Aram; Uz, and Hul, and Gether, and Mash.
24 Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
And Arpachshad begat Shelah; and Shelah begat Eber.
25 Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
And unto Eber were born two sons: the name of the one was Peleg; for in his days was the earth divided; and his brother’s name was Joktan.
26 Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
And Joktan begat Almodad, and Sheleph, and Hazarmaveth, and Jerah;
27 Hadoram, Uzal, Dikla,
and Hadoram, and Uzal, and Diklah;
28 Obal, Abimayel, Sheba,
and Obal, and Abimael, and Sheba;
29 Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
and Ophir, and Havilah, and Jobab: all these were the sons of Joktan.
30 Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
And their dwelling was from Mesha, as thou goest toward Sephar, the mountain of the east.
31 Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
These are the sons of Shem, after their families, after their tongues, in their lands, after their nations.
32 Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.
These are the families of the sons of Noah, after their generations, in their nations: and of these were the nations divided in the earth after the flood.

< Farawa 10 >