+ Farawa 1 >

1 A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
In the beginning God created the heavens and the earth.
2 To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
Now the earth was formless and empty, and darkness was on the surface of the watery depths. And God's Spirit was hovering over the surface of the waters.
3 Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
And God said, "Let there be light," and there was light.
4 Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
And God saw that the light was good. And God separated the light from the darkness.
5 Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
And God called the light Day, and the darkness he called Night. There was evening and there was morning, one day.
6 Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
And God said, "Let there be an expanse in the midst of the waters, and let it separate the waters from the waters." And it was so.
7 Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
And God made the expanse, and separated the waters which were under the expanse from the waters which were above the expanse.
8 Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
And God called the expanse Sky. And God saw that it was good. There was evening and there was morning, a second day.
9 Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
And God said, "Let the waters under the sky be gathered to one gathering, and let the dry land appear." And it was so. And the waters under the sky gathered to their gatherings, and the dry land appeared.
10 Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
And God called the dry land Earth, and the gatherings of the waters he called Seas. And God saw that it was good.
11 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
And God said, "Let the earth produce vegetation, plants yielding seed after its kind, and fruit trees bearing fruit with seed in it after its kind, on the earth." And it was so.
12 Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
And the earth brought forth vegetation, plants yielding seed after its kind, and fruit trees bearing fruit with seed in it after its kind, on the earth. And God saw that it was good.
13 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
There was evening and there was morning, a third day.
14 Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
And God said, "Let there be lights in the expanse of the sky for the illumination of the day, to give light on the earth, and to rule the day and the night, and to separate between the day and the night. And let them be for signs, and for seasons, and for days, and for years;
15 bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
and let them be for lights in the expanse of the sky to shine on the earth." And it was so.
16 Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
And God made the two great lights—the greater light to rule the day, and the lesser light to rule the night—and the stars.
17 Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
And God set them in the expanse of the sky to shine on the earth,
18 su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
and to rule over the day and over the night, and to divide the light from the darkness. And God saw that it was good.
19 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
There was evening and there was morning, a fourth day.
20 Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
And God said, "Let the waters swarm with swarms of living creatures, and let flying creatures fly above the earth in the open expanse of the sky." And it was so.
21 Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
And God created the large sea creatures, and every living creature that moves, with which the waters swarmed, after its kind, and every winged flying creature after its kind. And God saw that it was good.
22 Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
And God blessed them, saying, "Be fruitful, and multiply, and fill the waters in the seas, and let the flying creatures multiply on the earth."
23 Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
There was evening and there was morning, a fifth day.
24 Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
And God said, "Let the earth bring forth living creatures after its kind: tame animals, and crawling creatures, and wild animals of the earth after its kind." And it was so.
25 Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
And God made the wild animals of the earth after its kind, and the tame animals after its kind, and everything that crawls on the ground after its kind. And God saw that it was good.
26 Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
And God said, "Let us make humankind in our image, after our likeness. And let them have dominion over the fish of the sea, and over the flying creatures of the sky, and over the tame animals, and over all the wild animals of the earth, and over every creature that crawls on the earth." And it was so.
27 Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
And God created humankind in his own image. In God's image he created him; male and female he created them.
28 Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
And God blessed them, saying, "Be fruitful, and multiply, and fill the earth, and subdue it, and have dominion over the fish of the sea, and over the flying creatures of the sky, and over all the tame animals, and over all the wild animals of the earth, and over all the creatures that crawl on the earth."
29 Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
And God said, "Look, I have given you every plant yielding seed, which is on the surface of all the earth, and every tree, which bears fruit yielding seed. It will be your food.
30 Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
And to every wild animal of the earth, and to every tame animal of the earth, and to every flying creature of the sky, and to every creature that crawls on the earth, in which there is life, I have given every green plant for food."
31 Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.
And God saw everything that he had made, and look, it was very good. There was evening and there was morning, a sixth day.

+ Farawa 1 >