< Ezra 8 >

1 Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
Evo glavara obitelji s rodoslovljem koji su sa mnom pošli iz Babilona za vladavine kralja Artakserksa:
2 Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
Od Pinhasovih sinova: Geršom; od Itamarovih sinova: Daniel; od Davidovih sinova: Hatuš,
3 ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
Šekanijini sinovi; od sinova Paroševih: Zaharija i s njim upisanih muškaraca stotinu i pedeset;
4 daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
od Pahat-Moabovih sinova: Elijoenaj, sin Zerahjin, i s njim dvije stotine muškaraca;
5 daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
od Zatuovih sinova: Šekanija, sin Jahazielov, i s njim tri stotine muškaraca;
6 daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
od sinova Adinovih: Ebed, sin Jonatanov, i s njim pedeset muškaraca;
7 daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
od Elamovih sinova: Izaija, sin Atalijin, i s njim sedamdeset muškaraca;
8 daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
od Šefatjinih sinova: Zebadja, sin Mihaelov, i s njim osamdeset muškaraca;
9 daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
od Joabovih sinova: Obadja, sin Jehielov, i s njim dvije stotine i osamnaest muškaraca;
10 daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
od sinova Banijevih: Šelomit, sin Josifjin, i s njim stotinu i šezdeset muškaraca;
11 daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
od Bebajevih sinova: Zaharija, sin Bebajev, i s njim dvadeset i osam muškaraca;
12 daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
od Azgadovih sinova: Johanan, sin Hakatanov, i s njim stotinu i deset muškaraca;
13 zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
od posljednjih Adonikamovih sinova poimence: Elifelet, Jeiel i Šemaja, i s njima šezdeset muškaraca;
14 daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
i od sinova Bigvajevih: Utaj, sin Zabudov, i s njim sedamdeset muškaraca.
15 Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
Sabrao sam ih kod rijeke koja teče prema Ahavi. Utaborili smo se za tri dana ondje. Pregledao sam svjetovnjake i svećenike, ali nisam ondje našao ni jednog levita.
16 Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
Tada sam poslao glavare Eliezera, Ariela, Šemaju, Elnatana, Jariba, Elnatana, Natana, Zahariju, Mešulama i učitelje Jojariba i Elnatana
17 Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
i uputio sam ih Idonu, poglavaru mjesta Kasifje. Stavio sam u njihova usta riječi koje će reći Idonu i njegovoj braći koja su se nalazila u mjestu Kasifji da nam pribave sluge za Dom Boga našega.
18 Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
Milostiva ruka Boga našega bijaše nad nama i oni nam dovedoše razumna čovjeka između sinova Mahlija, sina Levijeva, sina Izraelova: Šerebju s njegovim sinovima i braćom - njih osamnaest.
19 Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
Još Hašabju i s njim njegova brata Izaiju, sina Merarijeva, i njihove sinove: njih dvadeset.
20 Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
A od poslužitelja koje su David i glavari postavili levitima da im služe: dvije stotine i dvadeset poslužitelja. Svi su bili poimence zabilježeni.
21 A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
Ja sam ondje, kraj rijeke Ahave, proglasio post: da bismo se ponizili pred Bogom svojim i od njega izmolili sretan put sebi, svojoj djeci i svemu blagu svojem.
22 Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
Jer bih se stidio moliti od kralja vojske i konjanika da nas štite putem od neprijatelja; izjavili smo, naprotiv, kralju: “Ruka je Boga našega ispružena da blagoslovi sve one koji ga traže; njegova snaga i gnjev njegov nad onima su koji ga ostavljaju.”
23 Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
I tako smo postili i molili Boga svoga na ovu nakanu, i on nas usliša.
24 Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
Izabrao sam dvanaest glavara svećeničkih, Šerebju i Hašabju, i s njima desetoricu njihove braće;
25 Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
izmjerih im srebro, zlato i posuđe, darove koje su kralj, njegovi savjetnici, velikaši i svi Izraelci darovali za Dom Boga našega.
26 Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
Izmjerih i stavih u njihove ruke šest stotina i pedeset talenata srebra, stotinu srebrnih posuda od po dva talenta, stotinu talenata zlata,
27 kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
dvadeset zlatnih čaša od tisuću darika i dva vrča od dobre pozlaćene mjedi, skupocjene kao zlato.
28 Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
I rekoh im: “Vi ste Jahvi posvećeni; ovo je posuđe posvećeno, ovo srebro i zlato dragovoljno je darovano Jahvi, Bogu otaca vaših.
29 Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
Pazite i čuvajte ovo sve dok ne izmjerite pred glavarima svećeničkim i pred levitima i glavarima obitelji Izraelovih u Jeruzalemu, u dvoranama Doma Jahvina.”
30 Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
Svećenici i leviti primiše, dakle, izmjereno srebro, zlato i posuđe da ga odnesu u Jeruzalem, u Dom Boga našega.
31 A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
Dvanaestog dana prvoga mjeseca krenusmo od rijeke Ahave da pođemo u Jeruzalem: ruka Boga našega bijaše nad nama; on nas je na putu štitio od napada neprijatelja i od pljačkaša.
32 Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
Stigli smo u Jeruzalem i ondje smo se tri dana odmarali.
33 A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
Četvrtoga dana izmjereno je srebro, zlato i posuđe u Domu Boga našega i predano je u ruke Merimotu, sinu Urijinu, s kojim je bio Eleazar, sin Pinhasov; a pred njima bijahu leviti: Jozabad, sin Ješuin, i Noadja, sin Binujev.
34 Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
Sve je bilo na broju i težini. Zabilježena je tada sveukupna težina. U to vrijeme
35 Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
oni koji su se vratili iz sužanjstva, povratnici, priniješe žrtvu paljenicu Bogu Izraelovu: dvanaest junaca za sav Izrael, devedeset i šest ovnova, sedamdeset i sedam janjaca, dvanaest jaraca za grijehe - sve to kao paljenicu Jahvi.
36 Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.
Zatim predaše kraljeve naredbe kraljevskim satrapima i upraviteljima s one strane Rijeke i oni pomogoše narod i Dom Božji.

< Ezra 8 >