< Ezra 6 >

1 Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
Thanne kyng Darius comaundide, and thei rekenyden in the biblet of bokis, that weren kept in Babiloyne.
2 Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
And o book was foundun in Egbatanys, which is a castel in the prouynce of Medena, and sich a sentence of the kyng was writun therynne.
3 A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
In the first yeer of kyng Cirus, Cirus the kyng demyde, that, `Goddis hows, which is in Jerusalem, schulde be bildid in the place where thei offren sacrifices, and that thei sette foundementis supportynge the heiythe of sixti cubitis, and the lengthe of sixti cubitis, thre ordris of stonys vnpolischid,
4 Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
and so ordris of newe trees. Sotheli costis schulen be youun of the kyngis hows.
5 Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
But also the goldun and siluerne vessels of Goddis temple, whiche Nabugodonosor took fro the temple of Jerusalem, and brouyte tho in to Babiloyne, be yoldun, and borun ayen in to the temple of Jerusalem, and in to her place, whiche also be set in the temple of God.
6 Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
Now therfor Tathannai, duyk of the cuntrei which is biyende the flood, and Starbusannai, and youre counseleris, Arphasacei, that ben byyende the flood, departe ye fer fro hem;
7 Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
and suffre ye, that thilke temple of God be maad of the duyk of Jewis, and of the eldre men of hem; and that thei bilde that hows of God in his place.
8 Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
But also it is comaundid of me, that that bihoueth to be maad of tho preestis of Jewys, that the hows of God be bildid, that is, that costis be youun bisili to tho men of the arke of the kyng, that is, of tributis, that ben youun of the contrei biyende the flood, lest the werk be lettid.
9 A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
That if it be nede, yyue thei bothe calues, and lambren, and kidis in to brent sacrifice to God of heuene; wheete, salt, and wyn, and oile, bi the custom of preestis that ben in Jerusalem, be youun to hem bi ech dai, that no pleynt be in ony thing.
10 domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
And offre thei offryngis to God of heuene; and preye thei for the lijf of the kyng and of hise sones.
11 Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
Therfor the sentence is set of me, that if ony man chaungith this comaundement, a tre be takun of his hows, and be reisid, and be he hangid therynne; sotheli his hows be forfetid.
12 Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
Forsothe God, that makith his name to dwelle there, distrie alle rewmes and puple, that holdith forth her hond to impugne and destrie thilke hows of God, which is in Jerusalem. I Darius haue demyd the sentence, which Y wole be fillid diligentli.
13 Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
Therfor Tathannai, duyk of the `cuntrei biyende the flood, and Starbusannai, and hise counseleris, diden execucioun, `ether filliden, so diligentli, bi that that kyng Darius hadde comaundid.
14 Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
Sotheli the eldre men of Jewis bildiden, and hadden prosperite, bi the profesie of Aggey, the profete, and of Zacarie, the sone of Ado; and thei bildiden, and maden, for God of Israel comaundide, and for Cirus, and Darius, and Artaxerses, kyngis of Persis, comaundiden;
15 An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
and thei performyden this hows of God `til to the thridde dai of the monethe Adar, which is the sixte yeer of the rewme of king Darius.
16 Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
Forsothe the sones of Israel, the preestis and dekenes, and the othere of the sones of transmygracioun, `that is, that camen fro transmigracioun, `ether caitifte, maden the halewyng of Goddis hows in ioie;
17 Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
and offriden, `in the halewyng of Goddis hows, an hundrid caluys, twei hundryd wetheris, foure hundrid lambren, twelue buckis of geet for the synne of al Israel, bi the noumbre of lynagis of Israel.
18 Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
And thei ordeyneden preestis in her ordris, and dekenes in her whilis, on the werkis of God in Jerusalem, as it is writun in the book of Moises.
19 A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
Forsothe the sones of transmygracioun maden pask, in the fourtenthe dai of the firste monethe.
20 Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
For the preestis and dekenes as o man weren clensid, alle weren clene for to offre pask to alle the sones of transmygracioun, and to her britheren preestis, and to hem silf.
21 Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And the sones of Israel eeten, that turneden ayen fro transmygracioun, and ech man eet, that hadde departid hym silf fro al the defoulyng of hethene men of the lond, for to seke the Lord God of Israel.
22 Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.
And thei maden solempnyte of therf looues seuene daies in gladnesse; for the Lord hadde maad hem glad, and hadde turned the herte of the kyng of Assur to hem, that he wolde helpe `her hondis in the werk of the hows of the Lord God of Israel.

< Ezra 6 >