< Ezekiyel 4 >

1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
«و تو نیز‌ای پسر انسان آجری بگیر و آن راپیش روی خود بگذار و شهر اورشلیم را برآن نقش نما.۱
2 Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
و آن را محاصره کن و در برابرش برجها ساخته، سنگری در مقابلش برپا نما و به اطرافش اردو زده، منجنیقها به هر سوی آن برپاکن.۲
3 Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
و تابه آهنین برای خود گرفته، آن را در میان خود و شهر، دیواری آهنین بگذار و روی خود رابر آن بدار و محاصره خواهد شد و تو آن رامحاصره کن تا آیتی به جهت خاندان اسرائیل بشود.۳
4 “Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
پس تو بر پهلوی چپ خود بخواب و گناه خاندان اسرائیل را بر آن بگذار. موافق شماره روزهایی که بر آن بخوابی، گناه ایشان را متحمل خواهی شد.۴
5 Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
و من سالهای گناه ایشان را مطابق شماره روزها یعنی سیصد و نود روز بر تونهاده‌ام. پس متحمل گناه خاندان اسرائیل خواهی شد.۵
6 “Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
و چون اینها را به انجام رسانیده باشی، بازبه پهلوی راست خود بخواب و چهل روزمتحمل گناه خاندان یهودا خواهی شد. هر روزی را به جهت سالی برای تو قرار داده‌ام.۶
7 Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
و بازوی خود را برهنه کرده، روی به محاصره اورشلیم بدار و به ضد آن نبوت کن.۷
8 Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
و اینک بندها بر تومی نهم و تا روزهای محاصره ات را به اتمام نرسانیده باشی از پهلو به پهلوی دیگرت نخواهی غلطید.۸
9 “Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
پس گندم و جو و باقلا و عدس و ارزن وجلبان برای خود گرفته، آنها را در یک ظرف بریزو خوراکی از آنها برای خود بپز و تمامی روزهایی که به پهلوی خود می‌خوابی، یعنی سیصد و نود روز آن را خواهی خورد.۹
10 Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
وغذایی که می‌خوری به وزن خواهد بود، یعنی بیست مثقال برای هر روز. وقت به وقت آن راخواهی خورد.۱۰
11 Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
و آب را به پیمایش یعنی سدس یک هین خواهی نوشید. آن را وقت به وقت خواهی نوشید.۱۱
12 Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
و قرصهای نان جو که می‌خوری، آنها را بر سرگین انسان در نظر ایشان خواهی پخت.۱۲
13 Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
و خداوند فرمود به همین منوال بنی‌اسرائیل نان نجس در میان امت هایی که من ایشان را به میان آنها پراکنده می‌سازم خواهندخورد.»۱۳
14 Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
پس گفتم: «آه‌ای خداوند یهوه اینک جان من نجس نشده و از طفولیت خود تا به حال میته یادریده شده را نخورده‌ام و خوراک نجس به دهانم نرفته است.»۱۴
15 Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
آنگاه به من گفت: «بدان که سرگین گاو را به عوض سرگین انسان به تو دادم، پس نان خود را بر آن خواهی پخت.»۱۵
16 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
و مرا گفت: «ای پسر انسان اینک من عصای نان را در اورشلیم خواهم شکست و نان را به وزن و عسرت خواهندخورد و آب را به پیمایش و حیرت خواهندنوشید.۱۶
17 domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.
زیرا که محتاج نان و آب خواهند شد وبه حیرت بر یکدیگر نظر خواهند انداخت و به‌سبب گناهان خود گداخته خواهند شد.۱۷

< Ezekiyel 4 >