< Ezekiyel 33 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then the word of Yahweh came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, yi magana da mutanen ƙasarka ka faɗa musu cewa, ‘Sa’ad da na kawo takobi a kan ƙasar, mutanen ƙasar kuwa suka zaɓi ɗaya daga cikin mutanensu suka mai da shi mai tsaro,
“Son of man, declare this to your people; say to them, 'When I bring a sword against any land, then the people of that land take one man from among themselves and make him a watchman for them.
3 ya kuma ga takobi yana zuwa a kan ƙasar ya kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane,
He looks for the sword as it comes on the land, and he blows his horn to warn the people!
4 in wani ya ji busar amma bai kula ba, takobin zai zo ya ɗauki ransa, jininsa kuwa zai zauna a kansa.
If the people hear the sound of the horn but do not pay attention, and if the sword comes and kills them, then each one's blood is on his own head.
5 Da yake ya ji ƙarar busar amma bai kula ba, jininsa zai zauna a kansa. Da a ce ya kula, da ya ceci kansa.
If someone hears the sound of the horn and pays no attention, his blood is on him; but if he pays attention, he will save his own life.
6 Amma a ce mai tsaron ya ga takobi yana zuwa bai kuwa busa ƙaho don yă faɗakar da mutane ba sai takobi ya zo ya ɗauki ran waninsu, za a kawar da wannan mutum saboda zunubinsa, amma zan nemi hakkin jinin mutumin a kan mai tsaron.’
However, if the watchman sees the sword as it is coming, but if he does not blow the horn, with the result that the people are not warned, and if the sword comes and takes anyone's life, then that person dies in his own sin, but I will require his blood from the watchman.'
7 “Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro bisa gidan Isra’ila; saboda haka ka ji abin da zan faɗa ka kuma gargaɗe su.
Now you yourself, son of man! I have made you a watchman for the house of Israel; you will hear the words from my mouth and warn them on my behalf.
8 Sa’ad da na ce wa mugu, ‘Ya mugun mutum, tabbatacce za ka mutu,’ kai kuma ba ka yi magana don ka juyar da shi daga hanyoyinsa ba, wannan mugun mutum zai mutu domin zunubinsa, zan kuma nemi hakkin jininsa a kanka.
If I say to a wicked person, 'Wicked one, you will surely die!' but if you do not announce this so as to warn the wicked about his way, then he who is wicked will die in his sin, but I will require his blood from your hand!
9 Amma in ka faɗakar da mugun mutumin don yă juye daga hanyoyinsa bai kuwa yi haka ba, zai mutu saboda zunubinsa, amma kai za ka kuɓutar da kanka.
But you, if you warn the wicked about his way, so that he might turn back from it, and if he does not turn back from his way, then he will die in his sin, but you yourself will have saved your own life.
10 “Ɗan mutum, faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da kuke cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuma lalacewa saboda su. Ta ƙaƙa za mu rayu?”’
So you, son of man, say to the house of Israel, 'You are saying this, “Our transgressions and our sins are on us, and we are decaying in them! How can we live?”'
11 Ka faɗa musu, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba na jin daɗin mutuwar mugu, amma a maimako haka ya fi su juye daga hanyoyinsu su rayu. Ku juye! Ku juye daga mugayen hanyoyinku! Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?’
Say to them, 'As I live—this is the Lord Yahweh's declaration—I do not delight in the death of the wicked, for if the wicked repents from his way, then he will live! Repent! Repent from your wicked ways! For why should you die, house of Israel?'
12 “Saboda haka, ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen ƙasarka, ‘Adalcin adali ba zai cece shi sa’ad da ya ƙi yin biyayya ba, kuma muguntar mugu ba za tă sa ya fāɗi sa’ad da ya juya daga gare ta ba. Adali, in ya yi zunubi, ba za a bari yă rayu saboda adalcinsa na dā ba.’
So now you, son of man, say to your people, 'The righteousness of a righteous person will not save him if he sins! The wickedness of a wicked person will not cause him to perish if he repents from his sin! For the righteous person will not be able to live because of his righteousness if he sins.
13 In na faɗa wa adali cewa tabbatacce zai rayu, amma sai ya dogara ga adalcinsa ya kuma aikata mugunta, babu ayyukan adalcinsa da za a tuna; zai mutu saboda muguntar da ya aikata.
If I say to the righteous, “He will surely live!” and if he trusts in his righteousness and then commits injustice, I will not call to mind any of his righteousness. He will die for the wickedness he committed.
14 Kuma in na ce wa mugu, ‘Tabbatacce za ka mutu,’ amma sai ya juye daga zunubinsa ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai,
So if I say to the wicked, “You will surely die,” but if he then repents from his sins and does what is just and right—
15 in ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya sata, ya kiyaye ƙa’idodin da suke ba da rai, ya daina yin mugunta, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
if he restores the loan guarantee that he wickedly demanded, or if he makes restitution for what he has stolen, and if he walks in the statutes that give life and no longer commits sin—then he will surely live. He will not die.
16 Babu wani zunubin da ya aikata da za a tuna da shi. Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai; tabbatacce zai rayu.
None of the sins that he has committed will be called to mind for him. He has acted justly and rightly, and so, he will surely live!
17 “Duk da haka mutanen ƙasarka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Alhali kuwa tasu ce ba daidai ba.
But your people say, “The way of the Lord is not fair!” but it is your ways that are not fair!
18 In adali ya juye daga adalcinsa ya yi mugunta, zai mutu saboda haka.
When the righteous person turns away from his righteousness and commits sin, then he will die in it!
19 Kuma in mugu ya juye daga muguntarsa ya aikata abin da yake gaskiya da kuma daidai, zai rayu ta yin haka.
When the wicked turns away from his wickedness and does what is just and righteous, he will live because of those things!
20 Duk da haka, ya gidan Isra’ila kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Amma zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”
But you people say, “The way of the Lord is not fair!” I will judge each of you according to his way, house of Israel!'”
21 A shekara ta goma sha biyu ta zaman bautanmu, a wata na goma a rana ta biyar, wani mutumin da ya gudu daga Urushalima ya zo wurina ya ce, “Birnin ya fāɗi!”
It happened in the twelfth year, on the fifth day of the tenth month of our captivity, that a fugitive came to me from Jerusalem and said, “The city has been captured!”
22 To a yamman da ya wuce kafin mutumin ya iso, hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma buɗe bakina kafin mutumin ya iso wurina da safe. Sai bakina ya buɗu ban kuma yi shiru ba.
The hand of Yahweh had been on me in the evening before the fugitive came, and my mouth was opened by the time that he came to me in the dawn. So my mouth was open; I was no longer mute!
23 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then the word of Yahweh came to me, saying,
24 “Ɗan mutum, mutanen da suke zama a waɗannan kufai a ƙasar Isra’ila suna cewa, ‘Ibrahim mutum ɗaya ne kaɗai, duk da haka Ibrahim ya mallaki ƙasar. Amma mu da muke da yawa; lalle an ba mu ƙasar ta zama mallakarmu.’
“Son of man, the ones inhabiting those ruins in the land of Israel are talking and say, 'Abraham was only one person, and he inherited the land, but we are many! The land has been given to us as a possession.'
25 Saboda haka ka faɗa musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kun ci nama da jini a cikinsa kuka kuma bauta wa gumakanku kuka zub da jini, kuna gani za ku mallaki ƙasar?
Therefore say to them, 'The Lord Yahweh says this: You eat blood, and you lift up your eyes towards your idols, then you pour out people's blood. Should you really possess the land?
26 Kun dogara ga takobinku, kuka aikata abubuwan banƙyama, kowannenku kuma ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa. Kuna gani za ku mallaki ƙasar?’
You have depended on your swords and have done disgusting things; each man defiles his neighbor's wife. Should you really possess the land?'
27 “Ka faɗa musu wannan, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa muddin ina raye, waɗanda aka rage a kufai za su fāɗi ga takobi, waɗanda suke bayan gari kuwa namun jeji za su cinye su, waɗanda suke a mafaka da kogwannin duwatsu annoba za tă kashe su.
You will say this to them, 'The Lord Yahweh says this: As I live, surely the ones in the ruins will fall by the sword, and I will give those in the fields to the living creatures as food, and those in fortresses and in caves will die of plagues.
28 Zan mai da ƙasar kango, kuma fariyar ƙarfinta zai ƙare, duwatsun Isra’ila za su zama kufai don kada wani ya ratsa su.
Then I will turn the land into a desolation and a horror, and the pride of its might will end, for the mountains of Israel will be deserted, and there will be no one to pass through them.'
29 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na mai da ƙasar kango saboda dukan abubuwan banƙyamar da suka yi.’
So they will know that I am Yahweh, when I make the land a desolation and a waste because of all the abominations that they have done.
30 “Game da kai kuma, ɗan mutum, mutanen ƙasarka suna magana da juna game da kai a katanga da kuma ƙofofin gidaje, suna ce wa juna, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’
So now you, son of man—your people are saying things about you beside the walls and the gates of the houses, and each says to one another—each man to his brother, 'Let us go and listen to the prophet's word that comes out from Yahweh!'
31 Mutanena sukan zo wurinka, yadda suka saba su zauna a gabanka don su saurari maganarka, amma ba sa aiki da abin da suka ji. Da bakunansu suna nuna ƙauna, amma zukatansu cike da haɗama suke don ƙazamar riba.
So my people will come to you, as they often do, and will sit in front of you and listen to your words, but they will not obey them. Right words are in their mouths, but their hearts are going after unjust profit.
32 Tabbatacce, gare su ba ka fi mai waƙar ƙauna da murya mai daɗi kana kuma yin kiɗa sosai ba, gama sukan ji maganarka amma ba sa amfani da ita.
For you are like a lovely song to them, a beautiful sound that is well played on a stringed instrument, so they will listen to your words, but none of them will obey them.
33 “Sa’ad da dukan wannan ya cika kuma zai cika ɗin, sa’an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”
So when all of this happens—behold! it will happen!—then they will know that a prophet has been among them.”

< Ezekiyel 33 >