< Ezekiyel 29 >

1 A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
In the tenth year, in the tenth month on the twelfth day of the month, the word of Yahweh came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
“Son of man, set your face against Pharaoh, the king of Egypt; prophesy against him and against all of Egypt.
3 Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
Declare and say, 'The Lord Yahweh says this: Behold! I am against you, Pharaoh, king of Egypt. You, the great sea monster that lurks in the midst of the river, that says, “My river is my own. I have made it for myself.”
4 Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
For I will place hooks in your jaw, and the fish of your Nile will cling to your scales; I will lift you up from the middle of your river along with all the fish of the river that cling to your scales.
5 Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
I will throw you down into the wilderness, you and all the fish from your river. You will fall on the open field; you will not be gathered nor lifted up. I will give you as food to the living things of the earth and to the birds of the heavens.
6 Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
Then all the inhabitants of Egypt will know that I am Yahweh, because they have been a reed stalk to the house of Israel.
7 Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
When they took hold of you in their hand, you broke and tore open their shoulder; and when they leaned on you, you were broken, and you caused their legs to be unsteady.
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
Therefore the Lord Yahweh says this: Behold! I will bring a sword against you. I will cut off both man and beast from you.
9 Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
So the land of Egypt will become desolate and a ruin. Then they will know that I am Yahweh, because the sea monster had said, “The river is mine, for I have made it.”
10 saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
Therefore, behold! I am against you and against your river, so I will give the land of Egypt over to desolation and waste, and you will become a wasteland from the Migdol to Syene and the borders of Cush.
11 Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
No man's foot will pass through it, and no wild animal's foot will pass through it. It will not be inhabited for forty years.
12 Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
For I will make the land of Egypt a desolation in the midst of uninhabited lands, and its cities in the midst of wasted cities will become a desolation for forty years; then I will scatter Egypt among the nations, and I will disperse them though the lands.
13 “‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
For the Lord Yahweh says this: At the end of forty years I will gather Egypt from the peoples among whom they were scattered.
14 Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
I will restore the fortunes of Egypt and bring them back to the region of Pathros, to the land of their origin. Then they will be a lowly kingdom there.
15 Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
It will be the lowliest of the kingdoms, and it will not be lifted up any more among the nations. I will diminish them so they will no longer rule over nations.
16 Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
The Egyptians will no longer be a reason for confidence for the house of Israel. Instead, they will be a reminder of the iniquity that Israel committed when they turned to Egypt for help. Then they will know that I am the Lord Yahweh.'”
17 A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then it came about in the twenty-seventh year on the first of the first month, that the word of Yahweh came to me, saying,
18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
“Son of man, Nebuchadnezzar the king of Babylon stationed his army to do hard work against Tyre. Every head was rubbed until it was made bald, and every shoulder was made raw. Yet he and his army received no payment from Tyre for the hard work that he carried out against it.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
Therefore the Lord Yahweh says this, 'Behold! I am giving the land of Egypt to Nebuchadnezzar the king of Babylon, and he will take away its wealth, plunder its possessions, and carry off all he finds there; that will be his army's wages.
20 Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
I have given him the land of Egypt as the wages for the work they did for me—this is the Lord Yahweh's declaration.
21 “A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
On that day I will make a horn sprout up for the house of Israel, and I make you speak in their midst, so that they will know that I am Yahweh.'”

< Ezekiyel 29 >