< Ezekiyel 28 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
耶和華的話又臨到我說:
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
「人子啊,你對泰爾君王說,主耶和華如此說: 因你心裏高傲,說:我是神; 我在海中坐神之位。 你雖然居心自比神, 也不過是人,並不是神!
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
看哪,你比但以理更有智慧, 甚麼祕事都不能向你隱藏。
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
你靠自己的智慧聰明得了金銀財寶, 收入庫中。
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
你靠自己的大智慧和貿易增添資財, 又因資財心裏高傲。
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
所以主耶和華如此說: 因你居心自比神,
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
我必使外邦人, 就是列國中的強暴人臨到你這裏; 他們必拔刀砍壞你用智慧得來的美物, 褻瀆你的榮光。
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
他們必使你下坑; 你必死在海中, 與被殺的人一樣。
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
在殺你的人面前你還能說「我是神」嗎? 其實你在殺害你的人手中, 不過是人,並不是神。
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
你必死在外邦人手中, 與未受割禮的人一樣, 因為這是主耶和華說的。」
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
耶和華的話臨到我說:
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
「人子啊,你為泰爾王作起哀歌,說主耶和華如此說: 你無所不備, 智慧充足,全然美麗。
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
你曾在伊甸上帝的園中, 佩戴各樣寶石, 就是紅寶石、紅璧璽、金鋼石、 水蒼玉、紅瑪瑙、碧玉、 藍寶石、綠寶石、紅玉,和黃金; 又有精美的鼓笛在你那裏, 都是在你受造之日預備齊全的。
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
你是那受膏遮掩約櫃的基路伯; 我將你安置在上帝的聖山上; 你在發光如火的寶石中間往來。
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
你從受造之日所行的都完全, 後來在你中間又察出不義。
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
因你貿易很多, 就被強暴的事充滿,以致犯罪, 所以我因你褻瀆聖地, 就從上帝的山驅逐你。 遮掩約櫃的基路伯啊, 我已將你從發光如火的寶石中除滅。
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
你因美麗心中高傲, 又因榮光敗壞智慧, 我已將你摔倒在地, 使你倒在君王面前, 好叫他們目睹眼見。
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
你因罪孽眾多, 貿易不公, 就褻瀆你那裏的聖所。 故此,我使火從你中間發出,燒滅你, 使你在所有觀看的人眼前變為地上的爐灰。
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
各國民中,凡認識你的, 都必為你驚奇。 你令人驚恐, 不再存留於世,直到永遠。」
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
耶和華的話臨到我說:
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
「人子啊,你要向西頓預言攻擊她,
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
說主耶和華如此說: 西頓哪,我與你為敵, 我必在你中間得榮耀。 我在你中間施行審判、顯為聖的時候, 人就知道我是耶和華。
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
我必使瘟疫進入西頓, 使血流在她街上。 被殺的必在其中仆倒, 四圍有刀劍臨到她, 人就知道我是耶和華。」
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
「四圍恨惡以色列家的人,必不再向他們作刺人的荊棘,傷人的蒺藜,人就知道我是主耶和華。」
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
主耶和華如此說:「我將分散在萬民中的以色列家招聚回來,向他們在列邦人眼前顯為聖的時候,他們就在我賜給我僕人雅各之地,仍然居住。
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
他們要在這地上安然居住。我向四圍恨惡他們的眾人施行審判以後,他們要蓋造房屋,栽種葡萄園,安然居住,就知道我是耶和華-他們的上帝。」

< Ezekiyel 28 >