< Ezekiyel 23 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Veio mais a mim a palavra do Senhor, dizendo:
2 “Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
Filho do homem, houve duas mulheres, filhas de uma mãe.
3 Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
Estas fornicaram no Egito; na sua mocidade fornicaram; ali foram apertados os seus peitos, e ali foram apalpados os seios da sua virgindade.
4 Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
E os seus nomes eram: Ohola, a mais velha, e Oholiba, sua irmã; e foram minhas, e pariram filhos e filhas; e, quanto aos seus nomes, Samaria é Ohola, e Jerusalém é Oholiba.
5 “Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
E fornicou Ohola, sendo minha; e enamorou-se dos seus amantes, dos assyrios, seus vizinhos,
6 waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
Vestidos de azul, prefeitos e magistrados, todos mancebos de cobiçar, cavaleiros montados a cavalo.
7 Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
Assim cometeu ela as suas fornicações com eles, os quais todos eram a flôr dos filhos da Assyria, e com todos os de quem se enamorava; com todos os seus ídolos se contaminou.
8 Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
E as suas fornicações, que trouxe do Egito, não as deixou; porque com ela se deitaram na sua mocidade, e eles apalparam os seios da sua virgindade, e derramaram sobre ela a sua fornicação.
9 “Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
Portanto a entreguei na mão dos seus amantes, na mão dos filhos da Assyria, de quem se enamorara.
10 Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
Estes descobriram a sua vergonha, levaram seus filhos e suas filhas, mas a ela mataram à espada; e foi afamada entre as mulheres, e nela exerceram os juízos.
11 “Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
O que vendo sua irmã Oholiba, corrompeu o seu amor mais do que ela, e as suas fornicações mais do que as fornicações de sua irmã
12 Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
Enamorou-se dos filhos da Assyria, dos prefeitos e dos magistrados seus vizinhos, vestidos com primor, cavaleiros que andam montados em cavalos, todos mancebos de cobiçar.
13 Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
E vi que se tinha contaminado; que o caminho de ambas era o mesmo.
14 “Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
E aumentou as suas fornicações, porque viu homens pintados na parede, imagens dos caldeus, pintadas de vermelho;
15 da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
Cingidos de cinto nos seus lombos, e tiaras largas tingidas nas suas cabeças, todos de parecer de capitães, à semelhança dos filhos de Babilônia em Chaldea, terra do seu nascimento.
16 Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
E se enamorou deles, vendo-os com os seus olhos: e lhes mandou mensageiros a Chaldea.
17 Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
Então vieram a ela os filhos de Babilônia para a cama dos amores, e a contaminaram com as suas fornicações: e ela se contaminou com eles; então apartou-se deles a alma dela.
18 Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
Assim descobriu as suas fornicações, e descobriu a sua vergonha: então a minha alma se apartou dela, como já se tinha apartado a minha alma de sua irmã.
19 Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
Porém multiplicou as suas fornicações, lembrando-se dos dias da sua mocidade, em que fornicara na terra do Egito.
20 A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
E enamorou-se dos seus amantes, cujas carnes são como carnes de jumentos, e cujo fluxo é como o fluxo de cavalos.
21 Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
Assim trouxeste à memória a enormidade da tua mocidade, quando os do Egito apalpavam os teus seios, por causa dos peitos da tua mocidade.
22 “Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
Por isso, ó Oholiba, assim diz o Senhor Jehovah: Eis que eu suscitarei contra ti os teus amantes, dos quais se tinha apartado a tua alma, e os trarei contra ti de em redor:
23 Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
Os filhos de Babilônia, e todos os caldeus de Pecod, e de Soa, e de Coa, e todos os filhos da Assyria com eles, mancebos de cobiçar, prefeitos e magistrados todos eles, capitães e homens afamados, todos eles montados a cavalo.
24 Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
E virão contra ti com carros, carretas e rodas, e com ajuntamento de povos; e se porão contra ti em redor com rodelas, e escudos, e capacetes: e porei diante deles o juízo, e julgar-te-ão segundo os teus juízos.
25 Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
E porei contra ti o meu zelo, e usarão de indignação contigo: o nariz e as orelhas te tirarão, e o que te ficar de resto cairá à espada: teus filhos e tuas filhas eles te tomarão, e o que ficar por último em ti será consumido pelo fogo.
26 Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
Também te despirão os teus vestidos, e te tomarão as tuas jóias de enfeite.
27 Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
Assim farei cessar em ti a tua enormidade e a tua fornicação da terra do Egito; e não levantarás os teus olhos para eles, nem te lembrarás mais do Egito.
28 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
Porque assim diz o Senhor Jehovah: Eis que eu te entregarei na mão dos que aborreces, na mão daqueles de quem se tinha apartado a tua alma.
29 Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
E te tratarão com ódio, e levarão todo o teu trabalho, e te deixarão nua e despida: e descobrir-se-á a vergonha da tua fornicação, e a tua enormidade, e as tuas fornicações.
30 sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
Estas coisas se te farão, porquanto tu fornicaste após os gentios, e porquanto te contaminaste com os seus ídolos.
31 Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
No caminho de tua irmã andaste; por isso te darei o seu copo na tua mão.
32 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
Assim diz o Senhor Jehovah: Beberás o copo de tua irmã, fundo e largo: servirás de riso e escarneio; ele leva muito.
33 Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
De embriaguez e de dor te encherás: o copo de tua irmã Samaria é copo de espanto e de assolação.
34 Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
Bebe-lo-ás pois, e esgota-lo-ás, e os seus cacos roerás, e os teus peitos arrancarás; porque eu o falei, diz o Senhor Jehovah.
35 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
Portanto, assim diz o Senhor Jehovah: Porquanto te esqueceste de mim, e me lançaste para traz das tuas costas, leva tu pois também a tua enormidade e as tuas fornicações.
36 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
E disse-me o Senhor: Filho do homem, porventura julgarias a Ohola e a Oholiba? mostra-lhes pois as suas abominações.
37 gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
Porque cometeram adultério, e sangue se acha nas suas mãos, e com os seus ídolos cometeram adultério, e até os seus filhos, que me geraram, fizeram passar pelo fogo por si, para os consumir.
38 Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
E ainda isto me fizeram: contaminaram o meu santuário no mesmo dia, e profanaram os meus sábados.
39 A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
Porque, havendo sacrificado seus filhos aos seus ídolos, vinham ao meu santuário no mesmo dia para o profanarem; e eis que assim fizeram no meio da minha casa.
40 “Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
E, o que mais é, enviaram uns homens, que haviam de vir de longe, aos quais fôra enviado um mensageiro, e eis que vieram, por amor dos quais te lavaste, coloriste os teus olhos, e te enfeitaste de enfeites.
41 Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
E te assentaste sobre um leito de honra, diante do qual estava uma mesa preparada: e puseste sobre ela o meu incenso e o meu óleo.
42 “Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
Havia com ela a voz de uma multidão satisfeita, e com varões da classe baixa foram trazidos beberrões do deserto; e puseram braceletes nas suas mãos, e corôas de esplendor nas suas cabeças.
43 Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
Então disse à envelhecida em adultérios: Agora deveras fornicarão as suas fornicações, como também ela.
44 Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
E entraram a ela, como quem entra a uma prostituta: assim entraram a Ohola e a Oholiba, mulheres infames.
45 Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
De maneira que homens justos eles as julgarão conforme o juízo das adulteras, e conforme o juízo das que derramam o sangue; porque adulteras são, e sangue há nas suas mãos.
46 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
Porque assim diz o Senhor Jehovah: Farei subir contra elas uma congregação, e as entregarei ao desterro e ao roubo.
47 Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
E a congregação as apedrejará com pedras, e as acutilarão com as suas espadas: a seus filhos e a suas filhas matarão, e as suas casas queimarão a fogo.
48 “Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
Assim farei cessar a infâmia da terra, para que se escarmentem todas as mulheres, e não façam conforme a vossa infâmia.
49 Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”
E a vossa infâmia carregarão sobre vós, e levareis os pecados dos vossos ídolos; e sabereis que eu sou o Senhor Jehovah.

< Ezekiyel 23 >