< Ezekiyel 23 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۱
2 “Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
«ای پسر انسان دو زن دختر یک مادربودند.۲
3 Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
و ایشان در مصر زنا کرده، در جوانی خودزناکار شدند. در آنجا سینه های ایشان را مالیدند وپستانهای بکارت ایشان را افشردند.۳
4 Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
و نامهای ایشان بزرگتر اهوله و خواهر او اهولیبه بود. وایشان از آن من بوده، پسران و دختران زاییدند. واما نامهای ایشان اهوله، سامره می‌باشد و اهولیبه، اورشلیم.۴
5 “Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
و اهوله از من رو تافته، زنا نمود و برمحبان خود یعنی بر آشوریان که مجاور او بودندعاشق گردید؛۵
6 waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
کسانی که به آسمانجونی ملبس بودند؛ حاکمان و سرداران که همه ایشان جوانان دلپسند و فارسان اسب‌سوار بودند.۶
7 Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
و به ایشان یعنی به جمیع برگزیدگان بنی آشور فاحشگی خود را بذل نمود و خود را از جمیع بتهای آنانی که بر ایشان عاشق می‌بود نجس می‌ساخت.۷
8 Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
وفاحشگی خود را که در مصر می‌نمود، ترک نکرد. زیرا که ایشان در ایام جوانیش با او همخواب می‌شدند و پستانهای بکارت او را افشرده، زناکاری خود را بر وی می‌ریختند.۸
9 “Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
لهذا من او رابه‌دست عاشقانش یعنی به‌دست بنی آشور که اوبر ایشان عشق می‌ورزید، تسلیم نمودم.۹
10 Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
که ایشان عورت او را منکشف ساخته، پسران ودخترانش را گرفتند. و او را به شمشیر کشتند که در میان زنان عبرت گردید و بر وی داوری نمودند.۱۰
11 “Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
«و چون خواهرش اهولیبه این را دید، درعشقبازی خویش از او زیادتر فاسد گردید وبیشتر از زناکاری خواهرش زنا نمود.۱۱
12 Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
و بر بنی آشور عاشق گردید که جمیع ایشان حاکمان وسرداران مجاور او بودند و ملبس به آسمانجونی و فارسان اسب‌سوار و جوانان دلپسند بودند.۱۲
13 Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
ودیدم که او نیز نجس گردیده و طریق هردوی ایشان یک بوده است.۱۳
14 “Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
پس زناکاری خود رازیاد نمود، زیرا صورتهای مردان که بر دیوارهانقش شده بود یعنی تصویرهای کلدانیان را که به شنجرف کشیده شده بود، دید.۱۴
15 da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
که کمرهای ایشان به کمربندها بسته و عمامهای رنگارنگ برسر ایشان پیچیده بود. و جمیع آنها مانند سرداران و به شبیه اهل بابل که مولد ایشان زمین کلدانیان است بودند.۱۵
16 Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
و چون چشم او بر آنها افتاد، عاشق ایشان گردید. و رسولان نزد ایشان به زمین کلدانیان فرستاد.۱۶
17 Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
و پسران بابل نزد وی در بسترعشق بازی درآمده، او را از زناکاری خود نجس ساختند. پس چون خود را از ایشان نجس یافت، طبع وی از ایشان متنفر گردید.۱۷
18 Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
و چون که زناکاری خود را آشکار کرد و عورت خود رامنکشف ساخت، جان من از او متنفر گردید، چنانکه جانم از خواهرش متنفر شده بود.۱۸
19 Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
امااو ایام جوانی خود را که در آنها در زمین مصر زناکرده بود به یاد آورده، باز زناکاری خود را زیادنمود.۱۹
20 A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
و بر معشوقه های ایشان عشق ورزید که گوشت ایشان، مثل گوشت الاغان و نطفه ایشان چون نطفه اسبان می‌باشد.۲۰
21 Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
و قباحت جوانی خود را حینی که مصریان پستانهایت را به‌خاطرسینه های جوانیت افشردند به یاد آوردی.۲۱
22 “Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
«بنابراین‌ای اهولیبه خداوند یهوه چنین می‌فرماید: اینک من عاشقانت را که جانت ازایشان متنفر شده است به ضد تو برانگیزانیده، ایشان را از هر طرف برتو خواهم آورد.۲۲
23 Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
یعنی پسران بابل و همه کلدانیان را از فقود و شوع وقوع. و همه پسران آشور را همراه ایشان که جمیع ایشان جوانان دلپسند و حاکمان و والیان و سرداران و نامداران هستند و تمامی ایشان اسب‌سوارند.۲۳
24 Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
و با اسلحه و کالسکه‌ها و ارابه‌ها وگروه عظیمی بر تو خواهند آمد و با مجن‌ها وسپرها و خودها تو را احاطه خواهند نمود. و من داوری تو را به ایشان خواهم سپرد تا تو را برحسب احکام خود داوری نمایند.۲۴
25 Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
و من غیرت خود را به ضد تو خواهم برانگیخت تا با تو به غضب عمل نمایند. و بینی و گوشهایت راخواهند برید و بقیه تو با شمشیر خواهند افتاد وپسران و دخترانت را خواهند گرفت و بقیه تو به آتش سوخته خواهند شد.۲۵
26 Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
و لباس تو را از توکنده، زیورهای زیبایی تو را خواهند برد.۲۶
27 Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
پس قباحت تو و زناکاریت را که از زمین مصرآورده‌ای، از تو نابود خواهم ساخت. و چشمان خود را بسوی ایشان بر نخواهی افراشت و دیگرمصر را به یاد نخواهی آورد.۲۷
28 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
زیرا خداوندیهوه چنین می‌گوید: اینک تو را به‌دست آنانی که از ایشان نفرت داری و به‌دست آنانی که جانت ازایشان متنفر است، تسلیم خواهم نمود.۲۸
29 Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
و با تواز راه بغض رفتار نموده، تمامی حاصل تو راخواهند گرفت و تو را عریان و برهنه وا خواهم گذاشت. تا آنکه برهنگی زناکاری تو و قباحت وفاحشه گری تو ظاهر شود.۲۹
30 sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
و این کارها را به توخواهم کرد، از این جهت که در عقب امت‌ها زنانموده، خویشتن را از بتهای ایشان نجس ساخته‌ای.۳۰
31 Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
و چونکه به طریق خواهر خودسلوک نمودی، جام او را به‌دست تو خواهم داد.۳۱
32 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
و خداوند یهوه چنین می‌فرماید: جام عمیق وبزرگ خواهر خود را خواهی نوشید. و محل سخریه و استهزا خواهی شد که متحمل آن نتوانی شد.۳۲
33 Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
و از مستی و حزن پر خواهی شد. از جام حیرت و خرابی یعنی از جام خواهرت سامره.۳۳
34 Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
و آن را خواهی نوشید و تا ته خواهی آشامید و خورده های آن را خواهی خایید وپستانهای خود را خواهی کند، زیرا خداوند یهوه می‌گوید که من این را گفته‌ام.۳۴
35 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
بنابراین خداوندیهوه چنین می‌فرماید: چونکه مرا فراموش کردی و مرا پشت سر خود انداختی، لهذا تو نیز متحمل قباحت و زناکاری خود خواهی شد.»۳۵
36 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
و خداوند مرا گفت: «ای پسر انسان! آیابراهوله و اهولیبه داوری خواهی نمود؟ بلکه ایشان را از رجاسات ایشان آگاه ساز.۳۶
37 gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
زیرا که زنا نموده‌اند و دست ایشان خون آلود است و بابتهای خویش مرتکب زنا شده‌اند. و پسران خودرا نیز که برای من زاییده بودند، به جهت آنها ازآتش گذرانیده‌اند تا سوخته شوند.۳۷
38 Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
و علاوه برآن این را هم به من کرده‌اند که در همانروز مقدس مرا بی‌عصمت کرده، سبت های مرا بی‌حرمت نموده‌اند.۳۸
39 A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
زیرا چون پسران خود را برای بتهای خویش ذبح نموده بودند، در همان روز به مقدس داخل شده، آن را بی‌عصمت نمودند و هان این عمل را در خانه من بجا آوردند.۳۹
40 “Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
بلکه نزدمردانی که از دور آمدند، فرستادید که نزد ایشان قاصدی فرستاده شد. و چون ایشان رسیدند، خویشتن را برای ایشان غسل دادی و سرمه به چشمانت کشیدی و خود را به زیورهایت آرایش دادی.۴۰
41 Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
و بر بستر فاخری که سفره پیش آن آماده بود نشسته، بخور و روغن مرا بر آن نهادی.۴۱
42 “Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
و در آن آواز گروه عیاشان مسموع شد. وهمراه آن گروه عظیم صابیان از بیابان آورده شدندکه دستبندها بر دستها و تاجهای فاخر بر سر هردوی آنها گذاشتند.۴۲
43 Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
و من درباره آن زنی که در زناکاری فرسوده شده بود گفتم: آیا ایشان الان بااو زنا خواهند کرد و او با ایشان؟۴۳
44 Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
و به اودرآمدند به نهجی که نزد فاحشه‌ها درمی آیند. همچنان به آن دو زن قباحت پیشه یعنی اهوله واهولیبه درآمدند.۴۴
45 Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
پس مردان عادل بر ایشان قصاص زنان زناکار و خونریز را خواهند رسانید، زیرا که ایشان زانیه می‌باشند و دست ایشان خون آلود است.۴۵
46 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
زیرا خداوند یهوه چنین می‌فرماید: من گروهی به ضد ایشان خواهم برانگیخت. و ایشان را مشوش ساخته، به تاراج تسلیم خواهم نمود.۴۶
47 Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
و آن گروه ایشان را به سنگها سنگسار نموده، به شمشیرهای خود پاره خواهند کرد. و پسران و دختران ایشان را کشته، خانه های ایشان را به آتش خواهند سوزانید.۴۷
48 “Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
وقباحت را از زمین نابود خواهم ساخت. پس جمیع زنان متنبه خواهند شد که مثل شما مرتکب قباحت نشوند.۴۸
49 Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”
و سزای قباحت شما را بر شماخواهند رسانید. و متحمل گناهان بتهای خویش خواهید شد و خواهید دانست که من خداوندیهوه می‌باشم.»۴۹

< Ezekiyel 23 >