< Ezekiyel 23 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the word of the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, an yi mata biyu,’yan matan mahaifiya guda.
Son of man, there were two women, daughters of one mother:
3 Suka zama karuwai a Masar, suka yi karuwanci tun daga ƙuruciyarsu. A wancan ƙasar an rungumi mamansu da ƙirjinsu na budurwanci.
and they went a-whoring in Egypt in their youth: there their breasts fell, there they lost their virginity.
4 Sunan babbar Ohola, ƙanuwarta kuwa Oholiba. Sun zama nawa suka kuma haifi’ya’ya maza da mata. Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.
And their names were Oola the elder, and Ooliba her sister: and they were mine, and bore sons and daughters: and [as for] their names, Samaria was Oola, and Jerusalem was Ooliba.
5 “Ohola ta shiga karuwanci yayinda take zamana; ta kuwa yi ta kai da kawowa da kwartayenta, Assuriyawa, mayaƙa
And Oola went a-whoring from me, and doted on her lovers, on the Assyrians that were her neighbors,
6 waɗanda suke saye da shunayya, gwamnoni da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha’awa, suna bisa kan dawakai.
clothed with purple, princes and captains; [they were] young men and choice, all horseman riding on horses.
7 Ta ba da kanta ga duk waɗanda suke masu ilimin Assuriya ta kuma ƙazantar da kanta da dukan gumaka na kowa da take kai da kawowa a cikinsu.
And she bestowed her fornication upon them; all were choice sons of the Assyrians: and on whomsoever she doted herself, with them she defiled herself in all [their] devices.
8 Ba ta bar karuwancin da ta fara a Masar ba, sa’ad da take budurwa maza sun kwana da ita, suka rungumi ƙirjinta suka kuma biya kwaɗayinsu a kanta.
And she forsook not her fornication with the Egyptians: for in her youth they committed fornication with her, and they deflowered her, and poured out their fornication upon her.
9 “Saboda haka na bashe ta ga kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu.
Therefore I delivered her into the hands of her lovers, into the hands of the children of the Assyrians, on whom she doted.
10 Suka tuɓe ta tsirara, suka kwashe’ya’yanta maza da mata suka kuma kashe ta da takobi. Ta kuwa zama abin karin magana a cikin mata, aka kuma yi mata hukunci.
They uncovered her shame: they took her sons and daughters, and slew her with the sword: and she became a byword among women: and they wrought vengeance in her for the sake of the daughters.
11 “Ƙanuwarta Oholiba kuwa ta ga wannan, duk da haka cikin kai da kawowarta da karuwancinta ta fi’yar’uwar lalacewa.
And her sister Ooliba saw [it], and she indulged in her fondness more corruptly than she, and in her fornication more than the fornication of her sister.
12 Ita ma ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, gwamnoni da manyan sojoji; mayaƙa masu saye da kayan yaƙi, suna bisa dawakai, dukansu samari ne masu bansha’awa.
She doted upon the sons of the Assyrian, princes and captains, her neighbours, clothed with fine linen, horsemen riding on horses; [they were] all choice young men.
13 Na ga cewa ita ma ta ƙazantar da kanta; dukansu biyu sun bi hanya guda.
And I saw that they were defiled, [that] the two [had] one way.
14 “Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a kan bango, siffofin sojojin Kaldiyawa suna cikin jajjayen riguna,
And she increased her fornication, and she saw men painted on the wall, likenesses of the Chaldeans painted with a pencil,
15 da ɗamara a gindinsu da rawuna a kansu suna kaɗawa falfal; dukansu sun yi kamar jarumawan kekunan yaƙin Babiloniyawa’yan Kaldiya.
having variegated girdles on their loins, having also richly dyed [attire] upon their heads; all had a princely appearance, the likeness of the children of the Chaldeans, of their native land.
16 Nan da nan da ta gan su, sai ta yi sha’awarsu ta aika da’yan aika zuwa wurinsu a Kaldiya.
And she doted upon them as soon as she saw them, and sent forth messengers to them into the land of the Chaldeans.
17 Sai Babiloniyawan suka zo wurinta, zuwa gadon soyayya, cikin kai da kawowarsu suka ƙazantar da ita. Bayan sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su.
And the sons of Babylon came to her, into the bed of rest, and they defiled her in her fornication, and she was defiled by them, and her soul was alienated from them.
18 Sa’ad da ta ci gaba da yin karuwancinta a fili ta kuma nuna tsiraicinta, sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita, kamar dai yadda na rabu da’yar’uwarta.
And she exposed her fornication, and exposed her shame: and my soul was alienated from her, even as my soul was alienated from her sister.
19 Duk da haka sai ta yi ta ƙara fasikanci tana tuna da kwanakin budurcinta, sa’ad da take karuwa a Masar.
And thou didst multiply thy fornication, so as to call to remembrance the days of thy youth, wherein thou didst commit whoredom in Egypt,
20 A can ta yi ta kai da kawowa da kwartayenta, waɗanda al’auransu kamar na jakuna ne waɗanda maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne.
and thou didst dote upon the Chaldeans, whose flesh is as the flesh of the asses, and their members [as] the members of horses.
21 Haka kika yi ta lalacin budurcinki, sa’ad da a Masar aka rungumi ƙirjinta aka tattaɓa nononta.
And thou didst look upon the iniquity of thy youth, [the things] which thou wroughtest in Egypt in thy lodgings, where were the breasts of thy youth.
22 “Saboda haka, Oholiba, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan zuga kwartayenki su yi gāba da ke, su waɗanda kika ji ƙyamarsu, zan kuma kawo su su yi gāba da ke daga kowane gefe,
Therefore, Ooliba, thus saith the Lord; Behold, I [will] stir up thy lovers against thee, from whom thy soul is alienated, and I will bring them upon thee round about,
23 Babiloniyawa da dukan Kaldiyawa, mutanen Fekod da Showa da Kowa, da dukan Assuriyawa, samari masu bansha’awa, dukan gwamnoni da manyan sojoji, hafsoshin keken yaƙin da mutane masu manyan matsayi, dukansu a bisa dawakai.
the children of Babylon, and all the Chaldeans, Phacuc, and Sue, and Hychue, and all the sons of the Assyrians with them; choice young men, governors and captains, all princes and renowned, riding on horses.
24 Za su yi gāba da ke da kayan yaƙi, kekunan yaƙi da kekunan doki da mutane masu yawa; za su ja dāgā a kanki a kowane gefe da garkuwoyi manya da ƙanana da kuma hulunan kwano. Zan miƙa ke gare su don hukunci, za su kuma hukunta ki bisa ga shari’arsu.
And they all shall come upon thee from the north, chariots and wheels, with a multitude of nations, shields and targets; and [the enemy] shall set a watch against thee round about: and I will set judgment before them, and they shall take vengeance on thee with their judgments.
25 Zan nuna fushin kishina a kanki, za su kuwa wulaƙanta ki da fushi. Za su yanke hancinki da kunnuwanki, waɗanda suka rage miki kuma za a kashe su da takobi. Za su kama’ya’yanki maza da mata, waɗanda suka rage miki kuwa za a ƙone su da wuta.
And I will bring upon thee my jealousy, and they shall deal with thee in great wrath: they shall take away thy nose and thine ears; and shall cast down thy remnant with the sword: they shall take thy sons and thy daughters; and thy remnant fire shall devour.
26 Za su tuɓe tufafinki su kuma kwashe kayan adonki masu kyau.
And they shall strip thee of thy raiment, and take [away] thine ornaments.
27 Ta haka zan tsai da marmari da kuma karuwancin da kika fara a Masar. Ba za ki dubi waɗannan abubuwa da marmari ko ki ƙara tuna da Masar ba.
So I will turn back thine ungodliness from thee, and thy fornication from the land of Egypt: and thou shalt not lift up thine eyes upon them, and shalt no more remember Egypt.
28 “Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina shirin miƙa ki ga waɗanda suke ƙinki, ga waɗanda kika ji ƙyamarsu kika rabu da su.
Wherefore thus saith the Lord God; Behold, I [will] deliver thee into the hands of those whom thou hatest, from whom thy soul is alienated.
29 Za su hukunta ki da ƙiyayya su kuma kwashe kome da kika yi wahalarsa. Za su bar ki tsirara tik, kunyan karuwancinki kuma zai tonu. Marmarinki da fasikancinki
And they shall deal with thee in hatred, and shall take all [the fruits] of thy labours and thy toils, and thou shalt be naked and bare: and the shame of thy fornication shall be exposed: and thy ungodliness and thy fornication
30 sun jawo miki wannan, domin ki yi ta kai da kawowa cikin ƙasashe kina ƙazantar da kanki da gumakansu.
brought this upon thee, in that thou wentest a-whoring after the nations, and didst defile thyself with their devices.
31 Kin bi hanyar’yar’uwarki; saboda haka zan sa kwaf nata a hannunki.
Thou didst walk in the way of thy sister; and I will put her cup into thine hands.
32 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Za ki sha kwaf na’yar’uwarki, kwaf wanda yake da girma da kuma zurfi; zai jawo dariya da kuma reni gama yana ɗauke da abubuwa da yawa.
Thus saith the Lord; Drink thy sister's cup, deep and large, and full, to cause complete drunkenness.
33 Za ki cika da buguwa da baƙin ciki, kwaf lalaci da kaɗaici, kwaf na’yar’uwarki Samariya.
And thou shalt be thoroughly weakened; and the cup of destruction, the cup of thy sister Samaria,
34 Za ki sha shi ki kuma lashe shi ƙaf; za ki buga shi da ƙasa ya yi rugu-rugu ki tsattsage nononki. Ni Ubangiji Mai Iko Duka na faɗa.
drink thou it, and I will take away her feasts and her new moons: for I have spoken [it], saith the Lord.
35 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa da yake kin manta da ni kika tura ni bayanki, dole ki sha sakamakon marmarinki da karuwancinki.”
Therefore thus saith the Lord; Because thou has forgotten me, and cast me behind thy back, therefore receive thou [the reward] of thine ungodliness and thy fornication.
36 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, za ka shari’anta Ohola da Oholiba? To, sai ka kalubalance su da ayyukansu masu banƙyama,
And the Lord said to me, Son of man, wilt thou not judge Oola and Ooliba? and declare to them their iniquities?
37 gama sun yi zina kuma jinin yana a hannuwansu. Sun yi zina da gumakansu; har suka miƙa’ya’yansu da suka haifa mini, su zama musu abinci.
For they have committed adultery, and blood was in their hands, they committed adultery with their devices, and they passed through the fire to them their children which they bore to me.
38 Sun kuma yi mini wannan. A lokaci guda sun ƙazantar da wuri mai tsarkina suka ɓata Asabbataina.
So long too as they did these things to me, they defiled my sanctuary, and profaned my sabbaths.
39 A ranar da suka miƙa’ya’yansu ga gumakansu, sai suka shiga wuri mai tsarkina suka kuma ƙazantar da shi. Abin da suka yi a gidana ke nan.
And when they sacrificed their children to their idols, they also went into my sanctuary to profane it: and whereas they did thus in the midst of my house;
40 “Sun ma aiki manzanni wa mutanen da suka zo daga nesa, kuma da suka iso kun yi wanka dominsu, kuka yi shafe-shafen idanunku, kuka kuma sa kayan adonku.
and whereas they did thus to the men that came from afar, to whom they sent messengers, and as soon as they came, immediately thou didst wash thyself, and didst paint thine eyes and adorn thyself with ornaments,
41 Kuka zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabanku wanda kun ajiye turare da maina.
and satest on a prepared bed, and before it [there was] a table set out, and [as for] mine incense and mine oil, they rejoiced in them,
42 “Surutun taron mutane marasa kula suna kewaye da ita; aka kawo Sabenawa daga hamada tare da mutane daga mashaya, suka sa mundaye a hannuwan macen da kuma’yar’uwarta suka kuma sa rawani masu kyau a kawunansu.
and they raised a sound of music, and [that] with men coming from the wilderness out of a multitude of men, and they put bracelets on their hands, and a crown of glory on their heads;
43 Sai na yi magana a kan wadda ta ƙare ƙarfi ta wurin karuwanci na ce, ‘Yanzu bari su yi amfani da ita kamar karuwa, gama abin da take ke nan.’
Therefore I said, Do they not commit adultery with these? and has she also gone a-whoring [after] the manner of a harlot?
44 Suka kuwa kwana da ita. Kamar yadda maza suke kwana ta karuwa, haka suka kwana da waɗannan lalatattun mata, Ohola da Oholiba.
And they went in to her, as [men] go in to a harlot; so they went in to Oola and to Ooliba to work iniquity.
45 Amma masu adalci za su hukunta su irin da akan yi wa matan da suka yi zina suka kuma yi kisa, domin su mazinata ne kuma jini yana a hannuwansu.
And they are just men, and shall take vengeance on them with the judgment of an adulteress and the judgment of blood: for they are adulteresses, and blood is in their hands.
46 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kawo taron mutane a kansu a kuma miƙa su don a firgitar da su a kuma washe su.
Thus saith the Lord God, Bring up a multitude upon them, and send trouble and plunder into the midst of them.
47 Taron mutanen za su jajjefe su, su kuma sassare su da takuba; za su kashe’ya’yansu maza da mata su kuma ƙone gidajensu.
And stone them with the stones of a multitude, and pierce them with their swords: they shall slay their sons and their daughters, and shall burn up their houses.
48 “Ta haka zan kawo ƙarshe ga lalaci a ƙasar, don dukan mata su ji gargaɗi kada kuma su kwaikwaye ku
And I will remove ungodliness out of the land, and all the women shall be instructed, and shall not do according to their ungodliness.
49 Za ku sha hukuncin lalacinku ku kuma ɗauki hakkin zunuban bautar gumaka. Sa’an nan za ku san cewa Ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.”
And your ungodliness shall be recompensed upon you, and ye shall bear the guilt of your devices: and ye shall know that I am the Lord.

< Ezekiyel 23 >