< Ezekiyel 21 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
2 “Ɗan mutum, ka kafa fuskarka gāba da Urushalima ka kuma yi wa’azi a kan wuri mai tsarki. Ka yi annabci gāba da ƙasar Isra’ila
Fils d’homme, tourne ta face contre Jérusalem, et distille [tes paroles] contre les sanctuaires, et prophétise contre la terre d’Israël,
3 ka faɗa mata, ‘Ga abin da Ubangiji ya ce ina gāba da ke. Zan ja takobina daga kubensa in karkashe adalai da mugaye daga cikinki.
et dis à la terre d’Israël: Ainsi dit l’Éternel: Voici, c’est à toi que j’en veux, et je tirerai mon épée de son fourreau, et je retrancherai de toi le juste et le méchant.
4 Domin zan karkashe adalai da kuma mugaye, ba zan rufe takobina a kan kowa daga kudu zuwa arewa ba.
Parce que je retrancherai de toi le juste et le méchant, à cause de cela mon épée sortira de son fourreau contre toute chair, du midi jusqu’au nord;
5 Sa’an nan duka mutane za su san cewa Ni Ubangiji na ja takobina daga kubensa; ba zai sāke koma kuma ba.’
et toute chair saura que moi, l’Éternel, j’ai tiré mon épée de son fourreau: elle n’y retournera plus.
6 “Saboda ka yi nishi, ɗan mutum! Yi nishi a gabansu da ajiyar zuciya da ɓacin rai.
Et toi, fils d’homme, gémis à te briser les reins, gémis avec amertume devant leurs yeux.
7 Kuma sa’ad da suka tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Domin labarun da suke fitowa. Kowace zuciya za tă narke kowane hannu kuma ya gurgunta; kowane ruhu zai sume kowane gwiwa kuma ta rasa ƙarfi kamar ruwa.’ Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Et il arrivera que, quand ils te diront: Pourquoi gémis-tu? tu diras: C’est à cause de la rumeur, car elle vient; et tout cœur sera défaillant, et toutes les mains deviendront lâches, et tout esprit faiblira, et tous les genoux se fondront en eau. Voici, elle vient, elle est là, dit le Seigneur, l’Éternel.
8 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
9 “Ɗan mutum, yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, “‘Takobi, takobi, wasasshe da kuma gogagge,
Fils d’homme, prophétise, et dis: Ainsi dit l’Éternel: Dis: L’épée, l’épée est aiguisée et aussi fourbie.
10 wasasshe don kisa, gogagge har yana walwal kamar walƙiya! “‘Kada ku yi farin ciki, hukunci yana zuwa, domin kowa ya ƙi jin abin da na yi gargaɗi a kai.
C’est afin qu’elle égorge bien, qu’elle est aiguisée; c’est pour briller comme l’éclair, qu’elle est fourbie. Ou bien nous réjouirions-nous, [disant]: Le sceptre de mon fils méprise tout bois?
11 “‘An ba da wannan takobi don a goge, don a kama da hannu; an washe shi aka kuma goge, shiryayye don a yi kisa da shi.
Et il l’a donnée à fourbir, pour qu’on la prenne dans la main; c’est une épée aiguisée, et elle est fourbie, pour la mettre dans la main de celui qui tue.
12 Ka yi kuka ka yi makoki, ɗan mutum, gama yana gāba da dukan sarakunan Isra’ila. An jefa su ga takobi tare da jama’ata. Saboda haka ku buga ƙirjinku.
Crie et hurle, fils d’homme! Car elle sera contre mon peuple, elle sera contre tous les princes d’Israël: ils sont livrés à l’épée avec mon peuple; c’est pourquoi frappe sur ta cuisse.
13 “‘Gwaji tabbatacce zai zo. Kuma a ce sandan Yahuda, wanda takobi ya ƙi, ya ci gaba? In ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
Car l’épreuve [est faite]; et quoi?… si même le sceptre méprisant n’existe plus? dit le Seigneur, l’Éternel.
14 “Saboda haka fa, ɗan mutum ka yi annabci ka kuma tafa hannuwanka. Bari takobi ya yi sara sau biyu, har sau uku ma. Takobin kisa ne, takobi ne don kisa mai girma, zai kewaye su a kowane gefe.
Et toi, fils d’homme, prophétise, et frappe tes mains l’une contre l’autre, et que [les coups de] l’épée redoublent jusqu’à la troisième fois; c’est l’épée des tués, l’épée qui a tué le grand, [et] qui les environne.
15 Domin zukata su narke da yawa kuma su fāɗi, na tsai da takobin kisa a dukan ƙofofinsu. Kash! A sa ya haska kamar walƙiya, ana riƙe da shi don kisa.
C’est afin que le cœur se fonde et que les occasions de chute soient multipliées, que j’envoie l’épée menaçante contre toutes leurs portes. Ah! elle est faite pour briller comme l’éclair, et affilée pour tuer.
16 Ya takobi, yi sara zuwa dama ka yi kuma zuwa hagu, duk inda aka juya ka.
Ramasse [tes forces], va à droite, tourne-toi, va à gauche, où que ta face soit dirigée.
17 Zan tafa hannuwana, fushina kuwa zai sauka. Ni Ubangiji na faɗa.”
Et moi aussi je frapperai mes mains l’une contre l’autre, et je satisferai ma fureur. Moi, l’Éternel, j’ai parlé.
18 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l’Éternel vint à moi, disant:
19 “Ɗan mutum, ka nuna hanyoyi biyu inda takobin sarkin Babilon zai bi, duka biyun su fara daga ƙasa guda. Ka kafa shaida inda hanyar za tă rabu zuwa cikin birni.
Et toi, fils d’homme, place devant toi deux chemins par où vienne l’épée du roi de Babylone: qu’ils partent tous deux du même pays; et fais-toi un indicateur, fais-le à l’entrée du chemin d’une ville.
20 Ka nuna hanya guda wadda takobi zai fāɗo wa Rabba ta Ammonawa ɗayan kuma da zai fāɗo a kan Yahuda da kuma Urushalima mai katanga.
Tu disposeras un chemin pour que l’épée vienne à Rabba des fils d’Ammon, et [un chemin] en Juda, [pour que l’épée vienne] à Jérusalem, la [ville] forte.
21 Gama sarkin Babilon zai tsaya a mararrabar hanya, a inda hanyar ta rabu biyu, don yă yi duba. Zai jefa ƙuri’a da kibiyoyinsa, zai nemi shawarar gumakansa, zai bincike hanta.
Car le roi de Babylone se tient au point d’embranchement de la route, à la tête des deux chemins, pour pratiquer la divination: il secoue les flèches, il interroge les théraphim, il examine le foie.
22 A hannunsa na dama ƙuri’a don Urushalima za tă fito, inda zai kafa dundurusai, ya ba da umarni kisa, a yi kururuwar yaƙi, a kafa dundurusai a kan ƙofofi, a gina mahaurai a kuma yi ƙawanya.
Dans sa droite est la divination touchant Jérusalem, pour placer des béliers, pour qu’on ouvre la bouche en cris de carnage, pour qu’on élève la voix en cris de guerre, pour placer des béliers contre les portes, pour élever des terrasses, pour bâtir des tours.
23 Zai zama kamar duban ƙarya ne ga waɗanda suka yi rantsuwar yin masa biyayya, amma zai tunashe su game da laifinsu ya kuma kama su.
Et ce sera pour eux, à leurs yeux, une divination fausse, pour eux qui se sont engagés par serment; mais lui, il rappellera le souvenir de l’iniquité, pour qu’ils soient pris.
24 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku mutanen nan kun tuna da laifinku ta wurin tawaye, kun kuma bayyana zunubanku cikin dukan abin da kuke yi, domin kun yi haka, za a kama ku.
C’est pourquoi, ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Parce que vous rappelez en mémoire votre iniquité, en ce que vos transgressions sont découvertes, de sorte que vos péchés paraissent dans toutes vos actions; parce que vous êtes rappelés en mémoire, vous serez pris par [sa] main.
25 “‘Ya kai ƙazantaccen mugu, yerima Isra’ila, wanda kwanansa ta zo, wanda lokacin hukuncinsa ya cika fal,
Et toi, profane, méchant prince d’Israël, dont le jour est venu au temps de l’iniquité de la fin,
26 ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka kunce rawanin, ka ɗauke rawanin nan. Ba zai zama kamar yadda yake ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da mai girma.
ainsi dit le Seigneur, l’Éternel: Ôte la tiare, et enlève la couronne; ce qui est ne sera plus. Élève ce qui est bas, et abaisse ce qui est élevé.
27 Hallaka! Hallaka! Zan hallaka shi! Ba za a maido da shi ba sai ya ga ainihin mai shi; gare shi zan bayar da shi.’
J’en ferai une ruine, une ruine, une ruine! Ceci aussi ne sera plus, jusqu’à ce que vienne celui auquel appartient le juste jugement, et je le lui donnerai.
28 “Kai kuma, ɗan mutum, ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da Ammonawa da kuma zarginsu. “‘Takobi, takobi, an ja don kisa, an goge don cinyewa yana haske kamar walƙiya!
Et toi, fils d’homme, prophétise, et dis: Ainsi dit le Seigneur, l’Éternel, touchant les fils d’Ammon et touchant leur opprobre; et tu diras: L’épée, l’épée est tirée, elle est fourbie pour la tuerie, pour dévorer, pour briller,
29 Duk da wahayin ƙarya game da kai, duban ƙarya game da kai, za a sa shi a wuyan mugaye waɗanda za a kashe, waɗanda kwanansu ta zo, waɗanda lokacin hukuncinsu ya cika fal.
pendant qu’ils ont pour toi des visions de vanité et qu’ils devinent pour toi le mensonge, pour te jeter sur les cous des méchants qui sont tués, dont le jour est venu au temps de l’iniquité de la fin.
30 “‘Ka mai da takobi a kubensa. A inda aka halicce ka, a ƙasar kakanninka, zan hukunta ka.
Remets-la dans son fourreau! Je te jugerai au lieu où tu fus créé, au pays de ton origine.
31 Zan zub da hasalata a kanka in hura maka wutar fushina; Zan ba da kai a hannun mugayen mutanen da suka gwanince a hallakarwa.
Je verserai sur toi mon indignation, je soufflerai contre toi le feu de mon courroux, et je te livrerai en la main d’hommes brutaux, artisans de destruction.
32 Za ka zama itacen wuta, za a zub da jininka a ƙasarka, ba za a ƙara tuna da kai ba; gama Ni Ubangiji na faɗa.’”
Tu seras pour le feu, pour être dévoré; ton sang sera au milieu du pays; on ne se souviendra pas de toi; car moi, l’Éternel, j’ai parlé.

< Ezekiyel 21 >