< Ezekiyel 12 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
The word of the LORD also came to me, saying,
2 ɗan mutum, kana zama a cikin mutane masu tawaye, Suna da idanun gani amma ba sa gani, suna da kunnuwan ji amma ba sa ji, gama’yan tawaye ne.
"Son of man, you dwell in the midst of the rebellious house, who have eyes to see, and do not see, who have ears to hear, and do not hear; for they are a rebellious house.
3 “Saboda haka ɗan mutum, ka tattara kayanka don zuwa zaman bauta, ka tashi da rana suna gani ka ƙaura a inda kake zuwa wani wuri. Mai yiwuwa za su gane, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
Therefore, you son of man, prepare your stuff for moving, and move by day in their sight; and you shall move from your place to another place in their sight: it may be they will consider, though they are a rebellious house.
4 Da rana, yayinda suke kallo, ka fid da kayanka da ka tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma, yayinda suke kallo, ka fita kamar yadda mutane masu tafiyar zaman bauta sukan yi.
You shall bring forth your baggage by day in their sight, as baggage for exile; and you shall go forth yourself at even in their sight, as when men go forth into exile.
5 Yayinda suke kallo, ka huda katanga ka fitar da kayanka daga ciki.
Dig through the wall in their sight, and carry your stuff out that way.
6 Ka sa su a kafaɗarka yayinda suke kallo ka kuma fitar da su da dare. Ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na mai da kai alama ga gidan Isra’ila.”
In their sight you shall bear it on your shoulder, and carry it forth in the dark; you shall cover your face, so that you do not see the land: for I have set you for a sign to the house of Israel."
7 Sai na yi kamar yadda aka umarce ni. Da rana na fitar da kayana da na tattara don zuwa zaman bauta. Sa’an nan da yamma na huda katanga da hannuwana. Na kwashe kayana da dare, na ɗauke su a kafaɗuna yayinda suke kallo.
I did so as I was commanded: I brought forth my stuff by day, as stuff for removing, and in the even I dug through the wall with my hand; I brought it forth in the dark, and bore it on my shoulder in their sight.
8 Da safe maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
In the morning came the word of the LORD to me, saying,
9 “Ɗan mutum, gidan’yan tawayen nan na Isra’ila ba su tambaye ka, ‘Me kake yi ba?’
"Son of man, has not the house of Israel, the rebellious house, said to you, 'What are you doing?'
10 “Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan abin da Allah ya yi magana a kai ya shafi sarki a Urushalima da kuma dukan gidan Isra’ila waɗanda suke a can.’
Say to them, 'Thus says the LORD: This burden concerns the prince in Jerusalem, and all the house of Israel among whom they are.'
11 Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku.’ “Kamar yadda na yi, haka za a yi da su. Za a kai su zaman bauta kamar kamammu.
Say, 'I am your sign: like as I have done, so shall it be done to them; they shall go into exile, into captivity.'
12 “Sarkin da yake a cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa da dare ya tafi, za a huda masa rami a katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada yă ga ƙasar.
"The prince who is among them shall bear on his shoulder in the dark, and shall go forth. He shall dig through the wall and carry it through: he shall cover his face, because he shall not see the land with his eyes.
13 Zan shimfiɗa masa ragata, za a kuwa kama shi da tarkona; zan kawo shi Babiloniya, ƙasar Kaldiyawa, amma ba zai gan ta ba, a can kuwa zai mutu.
My net also will I spread on him, and he shall be taken in my snare; and I will bring him to Babylon to the land of the Chaldeans; yet shall he not see it, though he shall die there.
14 Zan warwatsa dukan waɗanda suke kewaye da shi a dukan fuskokin iska, ma’aikatansa da dukan rundunoninsa, zan fafare su da takobin da aka zāre.
I will scatter toward every wind all who are around him to help him, and all his bands; and I will draw out the sword after them.
15 “Za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na watsar da su a cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe.
They shall know that I am the LORD, when I shall disperse them among the nations, and scatter them through the countries.
16 Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, yunwa da annoba, saboda a cikin al’umman da suka tafi su furta dukan ayyukansu masu banƙyama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”
But I will leave a few men of them from the sword, from the famine, and from the pestilence; that they may declare all their abominations among the nations where they come; and they shall know that I am the LORD."
17 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreover the word of the LORD came to me, saying,
18 “Ɗan mutum, ka yi rawar jiki yayinda kake cin abincinka, ka kuma yi makyarkyata don tsoro yayinda kake shan ruwanka.
"Son of man, eat your bread with quaking, and drink your water with trembling and with fearfulness;
19 Ka faɗa wa mutanen ƙasar cewa, ‘Ga abin Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa game da waɗanda suke zama a Urushalima da kuma cikin ƙasar Isra’ila. Za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da yake ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda suna zama a can.
and tell the people of the land, 'Thus says the LORD concerning the inhabitants of Jerusalem, and the land of Israel: They shall eat their bread with fearfulness, and drink their water in dismay, that her land may be desolate, and all that is in it, because of the violence of all those who dwell in it.
20 Garuruwan da mutane suna ciki za su zama kufai ƙasar kuma za tă zama kango. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
The cities that are inhabited shall be laid waste, and the land shall be a desolation; and you shall know that I am the LORD.'"
21 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of the LORD came to me, saying,
22 “Ɗan mutum, mene ne wannan karin magana da kuke da shi a ƙasar Isra’ila mai cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba’?
"Son of man, what is this proverb that you have in the land of Israel, saying, 'The days are prolonged, and every vision fails?'
23 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.’ Ka ce musu, ‘Kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi.
Tell them therefore, 'Thus says the LORD: I will make this proverb to cease, and they shall no more use it as a proverb in Israel'; but tell them, 'The days are at hand, and the fulfillment of every vision.
24 Gama ba za a ƙara ganin wahayin ƙarya ko a yi duba na daɗin baki a cikin mutanen Isra’ila ba.
For there shall be no more any false vision nor flattering divination within the house of Israel.
25 Amma Ni Ubangiji zan yi magana abin da na nufa, za tă kuwa tabbata ba tare da jinkiri ba. Gama cikin kwanakinku, kai gidan’yan tawaye, zan cika duk abin da na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
For I am the LORD; I will speak, and the word that I shall speak shall be performed; it shall be no more deferred: for in your days, rebellious house, will I speak the word, and will perform it,' says the LORD."
26 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Again the word of the LORD came to me, saying,
27 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila suna cewa, ‘Wahayin da yake gani na shekaru masu yawa ne nan gaba, yana kuma annabce-annabce game da wani zamani ne can.’
"Son of man, look, they of the house of Israel say, 'The vision that he sees is for many day to come, and he prophesies of times that are far off.'
28 “Saboda haka ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa ba wata maganata da za tă ƙara yin jinkiri; duk abin da na faɗa zai cika, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Therefore tell them, 'Thus says the LORD: None of my words shall be deferred any more, but the word which I shall speak shall be performed, says the LORD.'"

< Ezekiyel 12 >