< Ezekiyel 11 >

1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
Puis l'Esprit m'éleva, et me mena à la porte Orientale de la maison de l'Eternel qui regarde vers l'Orient; et voici vingt-cinq hommes à l'entrée de la porte; et je vis au milieu d'eux Jaazanja fils de Hazur, et Pélatja fils de Bénaja, les principaux du peuple.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
Et il me dit: fils d'homme, ceux-ci sont les hommes qui ont des pensées d'iniquité, et qui donnent un mauvais conseil dans cette ville;
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
En disant: ce n'est pas une chose prête; qu'on bâtisse des maisons; elle est la chaudière, et nous [sommes] la chair.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
C'est pourquoi prophétise contre eux, prophétise, fils d'homme.
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
L'Esprit donc de l'Eternel tomba sur moi, et me dit: parle. Ainsi a dit l'Eternel: vous parlez ainsi, maison d'Israël, et je connais toutes les pensées de votre esprit.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Vous avez multiplié vos gens tués dans cette ville; et vous avez rempli ses rues de gens que vous avez mis à mort.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
C'est pourquoi, ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: les gens que vous avez fait mourir, et que vous avez mis au milieu d'elle, sont la chair, et elle est la chaudière, mais je vous tirerai hors du milieu d'elle.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Vous avez eu peur de l'épée, mais je ferai venir l'épée sur vous, dit le Seigneur l'Etemel.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
Et je vous tirerai hors de la ville, je vous livrerai entre les mains des étrangers, et j'exécuterai mes jugements contre vous.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Vous tomberez par l'épée; je vous jugerai dans le pays d'Israël; et vous saurez que je suis l'Eternel.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
Elle ne vous sera point une chaudière, et vous ne serez point au dedans d'elle comme la chair; je vous jugerai dans le pays d'Israël.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
Et vous saurez que je suis l'Eternel; car vous n'avez point marché dans mes statuts, et vous n'avez point suivi mes ordonnances; mais vous avez agi selon les ordonnances des nations qui sont autour de vous.
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
Or il arriva comme je prophétisais, que Pélatja fils de Bénaja mourut; alors je me prosternai sur mon visage, et je criai à haute voix, et dis: ah! ah! Seigneur Eternel! t'en vas-tu consumer [entièrement] le reste d'Israël?
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
Fils d'homme, tes frères, tes frères, les hommes de ta parenté, et tous ceux de la maison d'Israël entièrement [sont ceux] auxquels les habitants de Jérusalem ont dit: éloignez-vous de l'Eternel, la terre nous a été donnée en héritage.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
C'est pourquoi dis-leur: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: quoique je les aie éloignés entre les nations, et que je les aie dispersés par les pays, je leur ai pourtant été comme un petit Sanctuaire dans les pays auxquels ils sont venus.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
C'est pourquoi dis-leur: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: aussi je vous recueillerai d'entre les peuples, et je vous rassemblerai des pays auxquels vous avez été dispersés, et je vous donnerai la terre d'Israël.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
Et ils y entreront, et ôteront hors d'elle toutes ses infamies, et toutes ses abominations.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
Et je ferai qu'ils n'auront qu'un cœur, et je mettrai au dedans d'eux un esprit nouveau; j'ôterai le cœur de pierre hors de leur chair, et je leur donnerai un cœur de chair.
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
Afin qu'ils marchent dans mes statuts; qu'ils gardent mes ordonnances, et qu'ils les fassent; et ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Mais quant à ceux dont le cœur va après le désir de leurs infamies et de leurs abominations, quant à ceux-là, je ferai tomber sur leur tête les peines que mérite leur conduite, dit le Seigneur l'Eternel.
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Puis les Chérubins élevèrent leurs ailes, et les roues qui étaient vis-à-vis d'eux [s'élevèrent aussi], et la gloire aussi du Dieu d'Israël qui était sur eux par dessus.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
Et la gloire de l'Eternel s'éleva du milieu de la ville, et s'arrêta sur la montagne qui est à l'Orient de la ville.
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
Puis l'Esprit m'enleva, et me transporta en Caldée, vers ceux qui avaient été emmenés captifs, [le tout] en vision par l'Esprit de Dieu. Et la vision que j'avais vue disparut de devant moi.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
Alors je dis à ceux qui avaient été emmenés captifs toutes les choses que l'Eternel m'avait fait voir.

< Ezekiyel 11 >