< Fitowa 24 >

1 Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
I reèe Mojsiju: izaði gore ka Gospodu ti i Aron i Nadav i Avijud i sedamdeset starješina Izrailjevih, i poklonite se izdaleka.
2 sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
I Mojsije sam neka pristupi ka Gospodu, a oni neka ne pristupe; i narod neka ne ide na gore s njim.
3 Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
I doðe Mojsije, i kaza narodu sve rijeèi Gospodnje i sve zakone. I odgovori narod jednijem glasom i rekoše: èiniæemo sve što je rekao Gospod.
4 Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
I napisa Mojsije sve rijeèi Gospodnje, i ustavši rano naèini oltar pod gorom i dvanaest stupova za dvanaest plemena Izrailjevih.
5 Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
I posla mladiæe izmeðu sinova Izrailjevih, koji prinesoše žrtve paljenice i prinesoše teoce na žrtve zahvalne Gospodu.
6 Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
I uzevši Mojsije polovinu krvi, metnu u zdjele, a polovinu krvi izli na oltar.
7 Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
I uze knjigu zavjetnu i proèita narodu. A oni rekoše: što je god rekao Gospod èiniæemo i slušaæemo.
8 Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
A Mojsije uze krv, i pokropi njom narod, i reèe: evo krv zavjeta, koji uèini Gospod s vama za sve rijeèi ove.
9 Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
Potom otide gore Mojsije i Aron, Nadav i Avijud, i sedamdeset starješina Izrailjevih.
10 suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
I vidješe Boga Izrailjeva, i pod nogama njegovijem kao djelo od kamena safira i kao nebo kad je vedro.
11 Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
I ne pruži ruke svoje na izabrane izmeðu sinova Izrailjevih, nego vidješe Boga, pa jedoše i piše.
12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
I reèe Gospod Mojsiju: popni se k meni na goru, i ostani ovdje, i daæu ti ploèe od kamena, zakon i zapovijesti, koje sam napisao, da ih uèiš.
13 Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
Tada usta Mojsije s Isusom, koji ga služaše, i izaðe Mojsije na goru Božiju.
14 Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
A starješinama reèe: sjedite tu dok se vratimo k vama; a eto Aron i Or s vama; ko bi imao što, neka ide k njima.
15 Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
I otide Mojsije na goru, a oblak pokri goru.
16 sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
I bijaše slava Gospodnja na gori Sinajskoj, i oblak je pokrivaše šest dana; a u sedmi dan viknu Mojsija ispred oblaka.
17 Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
I slava Gospodnja bješe po viðenju kao oganj koji sažiže na vrh gore pred sinovima Izrailjevim.
18 Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.
I Mojsije uðe usred oblaka, i pope se na goru; i osta Mojsije na gori èetrdeset dana i èetrdeset noæi.

< Fitowa 24 >